• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

JAMB Ta Haramta Wa Dalibar Da Ta Yi Sakamakon Bogi Sake Zana Jarabawa

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
JAMB Ta Haramta Wa Dalibar Da Ta Yi Sakamakon Bogi Sake Zana Jarabawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Shirya Jarabawar Share Fagen Shiga Jami’a (JAMB) ta haramtawa wata mai suna, Mmesoma Ejikeme, dalibar da ake zargi da fitar da sakamakon jarrabawar shiga manyan makarantun gaba da sakandire (UTME) zana jarrabawar har tsawon shekaru uku.

Wannan na kunshe ne cikin sanarwar da shugaban hukumar ta JAMB, Dakta Fabian Benjamin, ya fitar a ranar Lahadi.

  • Abbas Ya Sanar Da Manyan Shugabannin Majalisar Wakilai
  • Akpabio Ya Nada Bamidele, Ndume, Umahi Da Asiru Manyan Mukamai A Majalisar Dattawa

Hukumar wadda ta gano samamakon jarabawar da Mmesoma ta buga na bogi a ranar Lahadi, ta nanata cewa, tuni ta dakatar da sakamakon dalibar.

JAMB ta kuma bai wa ‘yan Nijeriya tabbacin cewa, ba a yi mata kutse a cikin manhajarta, ta adana sakamakon jarrabawar ba musamman ganin yadda wasu daliban suka yi kwafin sakamakon jarrabawar na bogi ba da wata mai suna na Asimiyu Mariam Omobolanle wadda ta zauna zana jararrabawar ta UTME a 2021, har ta samu makin da ya kai 138.

A cewar hukumar, “Za mu ci gaba da kare mutuncinmu, muna kuma son mu kara nanata bayaninmu na baya cewa, sakamakon na UTME da dalibar da ta gabatar, na cewa ta samu maki 138 a jarabawar UTME ta 2021 na bogi ne.”

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

Sanarwar ta kara da cewa, “Muna son mu bayyana cewa, ita kanta Mmesoma ta bayyana hakikanin asalin wadda ke da sakamakon jarrabawar wanda ta ke ikirarin, inda ake da sakamakon ya bayyana asalin wadda ke da sakamakon tun kafin ta bayyana sakamakon.

Hukumar ta kuma shawarci al’ummar gari da su yi kokari su kwafi tsarin QR na shaidar sakamakon jarabawar don su gane wa idanunsu asalin wanda ya mallaki sakamakon kafin a yi na boginsa.

A cewar sanarwar, “shin ta ya za a ce, daga cikin daliban da suka zauna zana jarabawar UTME a 2023 a ce Ejikeme Mmesoma kadai ce ta iya bayyana sakamakonta.

Hukumar ta ce, ba wannan ne lokaci na farko da irin wannan ta taba faruwa da hukumar ba, inda ta tunasar da al’ummar kasar nan cewa, a lokutan baya an kai karar hukumar a gaban kotu, inda daga baya su kansu lauyoyin suka nemi yafiyar hukumar kan tsayawar da suka yi wa wadanda suka shigar da hukumar karar a gaban kotu.

Sanarwar ta kara da cewa, wani abin takaicin shi ne, yadda wasu suka sa son rai wajen bai wa Ejikeme kariya, inda sanarwar ta ce, ya kamata irin wadannan mutane su sake yin tunani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DalibaJambSakamakon Bogi
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Sa-Kai Sun Kashe Mutum 6 A Zamfara

Next Post

An Tsinci Jariri A Raye A Bayan Mahaifiyarsa Awa 24 Bayan Kashe Ta

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

2 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

3 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

4 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

5 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

7 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

9 hours ago
Next Post
An Tsinci Jariri A Raye A Bayan Mahaifiyarsa Awa 24 Bayan Kashe Ta

An Tsinci Jariri A Raye A Bayan Mahaifiyarsa Awa 24 Bayan Kashe Ta

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.