ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

JAMB Ta Haramta Wa Dalibar Da Ta Yi Sakamakon Bogi Sake Zana Jarabawa

by Abubakar Abba
3 years ago
JAMB

Hukumar Shirya Jarabawar Share Fagen Shiga Jami’a (JAMB) ta haramtawa wata mai suna, Mmesoma Ejikeme, dalibar da ake zargi da fitar da sakamakon jarrabawar shiga manyan makarantun gaba da sakandire (UTME) zana jarrabawar har tsawon shekaru uku.

Wannan na kunshe ne cikin sanarwar da shugaban hukumar ta JAMB, Dakta Fabian Benjamin, ya fitar a ranar Lahadi.

  • Abbas Ya Sanar Da Manyan Shugabannin Majalisar Wakilai
  • Akpabio Ya Nada Bamidele, Ndume, Umahi Da Asiru Manyan Mukamai A Majalisar Dattawa

Hukumar wadda ta gano samamakon jarabawar da Mmesoma ta buga na bogi a ranar Lahadi, ta nanata cewa, tuni ta dakatar da sakamakon dalibar.

ADVERTISEMENT

JAMB ta kuma bai wa ‘yan Nijeriya tabbacin cewa, ba a yi mata kutse a cikin manhajarta, ta adana sakamakon jarrabawar ba musamman ganin yadda wasu daliban suka yi kwafin sakamakon jarrabawar na bogi ba da wata mai suna na Asimiyu Mariam Omobolanle wadda ta zauna zana jararrabawar ta UTME a 2021, har ta samu makin da ya kai 138.

A cewar hukumar, “Za mu ci gaba da kare mutuncinmu, muna kuma son mu kara nanata bayaninmu na baya cewa, sakamakon na UTME da dalibar da ta gabatar, na cewa ta samu maki 138 a jarabawar UTME ta 2021 na bogi ne.”

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sanarwar ta kara da cewa, “Muna son mu bayyana cewa, ita kanta Mmesoma ta bayyana hakikanin asalin wadda ke da sakamakon jarrabawar wanda ta ke ikirarin, inda ake da sakamakon ya bayyana asalin wadda ke da sakamakon tun kafin ta bayyana sakamakon.

Hukumar ta kuma shawarci al’ummar gari da su yi kokari su kwafi tsarin QR na shaidar sakamakon jarabawar don su gane wa idanunsu asalin wanda ya mallaki sakamakon kafin a yi na boginsa.

A cewar sanarwar, “shin ta ya za a ce, daga cikin daliban da suka zauna zana jarabawar UTME a 2023 a ce Ejikeme Mmesoma kadai ce ta iya bayyana sakamakonta.

Hukumar ta ce, ba wannan ne lokaci na farko da irin wannan ta taba faruwa da hukumar ba, inda ta tunasar da al’ummar kasar nan cewa, a lokutan baya an kai karar hukumar a gaban kotu, inda daga baya su kansu lauyoyin suka nemi yafiyar hukumar kan tsayawar da suka yi wa wadanda suka shigar da hukumar karar a gaban kotu.

Sanarwar ta kara da cewa, wani abin takaicin shi ne, yadda wasu suka sa son rai wajen bai wa Ejikeme kariya, inda sanarwar ta ce, ya kamata irin wadannan mutane su sake yin tunani.

JAMB
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
An Tsinci Jariri A Raye A Bayan Mahaifiyarsa Awa 24 Bayan Kashe Ta

An Tsinci Jariri A Raye A Bayan Mahaifiyarsa Awa 24 Bayan Kashe Ta

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.