• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

by Rabi'u Ali Indabawa
1 month ago
in Labarai
0
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Makarantun Gaba da Sakandire (JAMB) ta kaddamar da wani kwamitin musamman domin bincikar al’amuran amfani da fasaha wajen yin magudin jarabawa da aka gano a yayin jarabawar UTME ta 2025.

Yayin kaddamar da Kwamitin Musamman Mai Mambobi 23 Kan Laifukan Jarabawa a ranar Litinin a Abuja, Shugaban JAMB, Farfesa Ishak Oloyede, ya nuna damuwa kan kara kwarewar masu magudin jarabawa, inda ya bayyana cewa sakamakon dalibai 6,458 na nan karkashin bincike bisa zargin shiga cikin magudin zamani na fasaha.

  • EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
  • Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

“Wannan shekarar mun gamu da abubuwa masu ban mamaki da dama, kuma mun ji zai fi kyau idan muka fadada hanyoyinmu. Muna kuma da yakinin cewa Allah ya albarkaci wannan kasa da tarin albarkatu da za mu iya amfana da su,” in ji Oloyede.

Oloyede ya jaddada cewa akwai bukatar daukar gaggawar mataki domin kare ingancin jarabawa.

“Magudin jarabawa wani abu ne da dole mu yi yaki da shi da kowace digon jinin da ke jikimmu,” in ji shi, yana gargadin cewa idan ba a shawo kan wannan matsala ba, zai iya lalata fannoni da dama tare da bata sunan Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Oloyede ya bayyana cewa an tura al’amuran “na al’ada” guda 141 na magudin jarabawa zuwa ga kwamitin ladabtarwa na JAMB, yana mai kara da cewa wannan sabon kwamiti zai yi aiki da “laifuka na musamman,” irin su hada hotuna (image blending), kirkirar rashin kwayar halitta (albinism falsification), hada yatsu (finger pairing), da kuma kokarin karya tsarin sadarwar Local Area Network na wasu cibiyoyin CBT.

Ya jera ayyukan da aka dora wa kwamitin, wanda suka hada da binciken dukkan al’amuran hada hotuna (image blending), hada yatsu (finger blending), karya da’awar rashin kwayar halitta (albinism) da kuma kirkirar sakamako a jarabawar 2025.

Haka kuma, gano hanyoyi, dabaru, kayan aiki da fasahohin da aka yi amfani da su wajen aikata wadannan laifuka, nazarin manufofin jarabawa da na rajista na yanzu da kuma bayar da shawarwari kan inganta su.

Bugu da kari, an dora wa kwamitin alhakin tantance ko wadanda ake zargi dalibai 6,458, ban da wadanda ke cikin rukuni na albinism, suna da hannu ko a’a, saboda sakamakonsu na nan a dakace.

Kwamitin zai kuma “ba da shawarar hukunci ko ladabtarwa da suka dace ga duk wani mutum ko rukuni da aka samu da laifi.”

“Ku gabatar da tsari mai wayewa domin gano, dakile da kuma hana magudin jarabawa da fasaha ta zamani ke taimakawa a nan gaba.

“Kuma ku yi la’akari ku bayar da shawara kan duk wata matsala da ta shafi wadannan al’amura,” in ji shi.

Kwamitin na da makonni uku bayan kaddamarwa don gabatar da rahoton aikinsa.

“Mun zabi makonni uku ne saboda an ce adalci da aka jinkirta tamkar adalci da aka hana ne.

“A cikin kusan makonni hudu, za a rufe karbar dalibai. Kuma muna ganin wadanda ba a same su da laifi ba su sami damar su,” in ji Oloyede.

Shugaban Kwamitin, Dakta Jake Epele, ya yaba da jagorancin Oloyede tare da yin alkawarin cewa kwamitin zai yi aiki tukuru wajen cika wannan aiki.

Mambobin kwamitin sun hada da Farfesa Muhammad Bello, Farfesa Samuel Odewummi, Farfesa Chinedum Nwajiuba, Farfesa Tanko Ishaya, Farfesa Ibe Ifeakandu, Tsohon Kwamishinan ‘Yansanda Fatai Owoseni, Dakta Chuks Okpaka na Microsoft Africa, da Shugaban Kungiyar Daliban Nijeriya (NANS), tare da wasu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Jamb
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Next Post

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

6 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

7 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

9 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

12 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

14 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

15 hours ago
Next Post
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.