ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

by Rabi'u Ali Indabawa
4 months ago
Jamb

Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Makarantun Gaba da Sakandire (JAMB) ta kaddamar da wani kwamitin musamman domin bincikar al’amuran amfani da fasaha wajen yin magudin jarabawa da aka gano a yayin jarabawar UTME ta 2025.

Yayin kaddamar da Kwamitin Musamman Mai Mambobi 23 Kan Laifukan Jarabawa a ranar Litinin a Abuja, Shugaban JAMB, Farfesa Ishak Oloyede, ya nuna damuwa kan kara kwarewar masu magudin jarabawa, inda ya bayyana cewa sakamakon dalibai 6,458 na nan karkashin bincike bisa zargin shiga cikin magudin zamani na fasaha.

  • EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
  • Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

“Wannan shekarar mun gamu da abubuwa masu ban mamaki da dama, kuma mun ji zai fi kyau idan muka fadada hanyoyinmu. Muna kuma da yakinin cewa Allah ya albarkaci wannan kasa da tarin albarkatu da za mu iya amfana da su,” in ji Oloyede.

ADVERTISEMENT

Oloyede ya jaddada cewa akwai bukatar daukar gaggawar mataki domin kare ingancin jarabawa.

“Magudin jarabawa wani abu ne da dole mu yi yaki da shi da kowace digon jinin da ke jikimmu,” in ji shi, yana gargadin cewa idan ba a shawo kan wannan matsala ba, zai iya lalata fannoni da dama tare da bata sunan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Oloyede ya bayyana cewa an tura al’amuran “na al’ada” guda 141 na magudin jarabawa zuwa ga kwamitin ladabtarwa na JAMB, yana mai kara da cewa wannan sabon kwamiti zai yi aiki da “laifuka na musamman,” irin su hada hotuna (image blending), kirkirar rashin kwayar halitta (albinism falsification), hada yatsu (finger pairing), da kuma kokarin karya tsarin sadarwar Local Area Network na wasu cibiyoyin CBT.

Ya jera ayyukan da aka dora wa kwamitin, wanda suka hada da binciken dukkan al’amuran hada hotuna (image blending), hada yatsu (finger blending), karya da’awar rashin kwayar halitta (albinism) da kuma kirkirar sakamako a jarabawar 2025.

Haka kuma, gano hanyoyi, dabaru, kayan aiki da fasahohin da aka yi amfani da su wajen aikata wadannan laifuka, nazarin manufofin jarabawa da na rajista na yanzu da kuma bayar da shawarwari kan inganta su.

Bugu da kari, an dora wa kwamitin alhakin tantance ko wadanda ake zargi dalibai 6,458, ban da wadanda ke cikin rukuni na albinism, suna da hannu ko a’a, saboda sakamakonsu na nan a dakace.

Kwamitin zai kuma “ba da shawarar hukunci ko ladabtarwa da suka dace ga duk wani mutum ko rukuni da aka samu da laifi.”

“Ku gabatar da tsari mai wayewa domin gano, dakile da kuma hana magudin jarabawa da fasaha ta zamani ke taimakawa a nan gaba.

“Kuma ku yi la’akari ku bayar da shawara kan duk wata matsala da ta shafi wadannan al’amura,” in ji shi.

Kwamitin na da makonni uku bayan kaddamarwa don gabatar da rahoton aikinsa.

“Mun zabi makonni uku ne saboda an ce adalci da aka jinkirta tamkar adalci da aka hana ne.

“A cikin kusan makonni hudu, za a rufe karbar dalibai. Kuma muna ganin wadanda ba a same su da laifi ba su sami damar su,” in ji Oloyede.

Shugaban Kwamitin, Dakta Jake Epele, ya yaba da jagorancin Oloyede tare da yin alkawarin cewa kwamitin zai yi aiki tukuru wajen cika wannan aiki.

Mambobin kwamitin sun hada da Farfesa Muhammad Bello, Farfesa Samuel Odewummi, Farfesa Chinedum Nwajiuba, Farfesa Tanko Ishaya, Farfesa Ibe Ifeakandu, Tsohon Kwamishinan ‘Yansanda Fatai Owoseni, Dakta Chuks Okpaka na Microsoft Africa, da Shugaban Kungiyar Daliban Nijeriya (NANS), tare da wasu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Next Post
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.