Daraktan ofishin kula da harkokin wajen kasar Sin na kwamitin kolin JKS Wang Yi, ya gana da ministan harkokin wajen Gabon Hermann Immongault, yau Litinin a birnin Beijing.
Da yake bayyana aminci a siyasance dake tsakanin Sin da Gabon a matsayin muhimmiyar fa’idar dangantakarsu, Wang Yi ya ce a shirye Sin take su ci gaba da goyon bayan juna wajen kare muradunsu da inganta hadin gwiwa a karin fannoni da manyan matakai da kuma hada hannu wajen daukaka ka’idojin huldar kasa da kasa.
A nasa bangare, Hermann Immongault, ya ce Gabon na yabawa gudunmuwar da Sin ke bayarwa ga zaman lafiya da ci gaban duniya, haka kuma tana godiya da jerin shirye-shiryen hadin gwiwa da Sin ke gabatarwa kan hadin gwiwarta da Afrika. A cewarsa, a shirye Gabon take ta hada hannu da Sin wajen inganta gina al’umma mai makoma ta bai daya ta Sin da Afrika. (Fa’iza)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp