ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Binani Ta Maka INEC A Kotu Kan Soke Ayyana Ta A Matsayin Wadda Ta Lashe Zaben Gwamnan Adamawa

by Sadiq
3 years ago
Binani

Aisha Dahiru, wadda aka fi sani da Binani, ‘yar takarar jam’iyyar APC a zaben gwamnan Adamawa, ta sake kai karar hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC).

Kamar yadda aka ruwaito a baya cewa INEC ta soke shelanta ta a matsayin gwamnan Adamawa a zaben gwamna da aka yi a ranar 18 ga Maris.

  • Abba Ya Sake Nada Sheikh Daurawa Shugaban Hisbah Ta Kano
  • Fisinjoji 20 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Hanyar Legas

Binani, wadda lauyanta, Michael Aondoaka, SAN, ya wakilta, ta gabatar da sabuwar kara a gaban mai shari’a Donatus Okorowo na babbar kotun tarayya da ke Abuja.

ADVERTISEMENT

A cikin karar mai lamba FHC/ABJ/CS/935/2023, ‘yar takarar jam’iyyar APC ta bayyana INEC, jam’iyyar PDP, da dan takararta, Gwamna Ahmadu Fintiri, a matsayin wadanda ta ke kara.

Binani na neman a binciki hukuncin da INEC ta yanke na sauya shelarta na farko a matsayin wadda ta lashe zaben da Kwamishinan Zabe na jihar, Hudu Yunusa-Ari ya yi.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

A yayin sauraren karar a ranar Litinin, Aondoaka ya bayar da hujjar cewa kotun sauraren kararrakin zabe ce ke da hurumin tantance makomar wadda yake karewa, inda ya ambaci sashe na 149 na dokar zabe na 2022.

Ya bayyana damuwarsa cewa matakin da INEC ta dauka zai hana Binani tanade-tanade da ke karkashin sashe na 285(6), wanda ya ba da damar kwanaki 180 don warware karar da ta shigar a gaban kotun a ranar 6 ga watan Mayu.

Aondoaka ya sanar da kotun cewa a baya an shigar da irin wannan kara a gaban mai shari’a Inyang Ekwo, wanda ya umarci Binani da ta garzaya kotun don wani lamari da ya shafi zabe.

Don haka, Aondoaka ya nemi a sake duba matakin na INEC kuma ya ba da wani aiki don nuna cewa karar da ake yi yanzu ba ta da tushe.

Ya tabbatar da cewa a shirye suke su biya duk wata tara idan har kotu ta ga cewa karar ba ta da tushe.

Mai shari’a Okorowo ya dage ci gaba da sauraren karar bayan ya saurari hujjojin Aondoaka.

Idan dai ba a manta ba Binani ta janye karar da ta shigar gaban mai shari’a Ekwo a ranar 26 ga watan Afrilu biyo bayan ayyana gwamna Fintiri a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna.

Lauyan Binani, Mohammed Sheriff, ya gabatar da sanarwar dakatar da shi kuma ya bukaci kotu ta soke karar.

Sai dai mai shari’a Ekwo ya tunatar da Sheriff hukuncin da kotun ta bayar tun farko, inda ya bukaci ya yi magana ko kotu takori shari’ar.

Alkalin ya yanke shawarar yin watsi da batun, bayan da Sheriff ya kasa bi umarnin.

Ida tuna cewa da sanyin safiyar Lahadi, 16 ga Afrilu, 2023, ‘yan Nijeriya suka kadu da ayyana Sanata Aishatu Dahiru Ahmed a matsayin wadda ta lashe zaben gwamnan jihar Adamawa da shugaban hukumar zaben jihar, Ari ya yi.

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Next Post
Ya Dace Amurka Ta Dauki Hakikanin Matakai Domin Karfafa Hadin Gwiwa Da Sin

Ya Dace Amurka Ta Dauki Hakikanin Matakai Domin Karfafa Hadin Gwiwa Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.