• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyar PDP A Kebbi Ta Shirya Tarbar Dan Takarar Shugaban Kasa, Atiku Abubakar

by Sulaiman and Umar Faruk
3 years ago
PDP

Jam’iyyar PDP reshen jihar Kebbi ta bayyana cewa ta shirya tsaf domin tarbar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Atiku Abubakar, GCON, a ranar 12 ga watan Nuwamba a jihar.

Da yake jawabi ga manema labarai a Birnin Kebbi, babban birnin jihar, Barista Kabiru Tanimu Turaki SAN, mamba a kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP (BOT) ya ce makasudin taron nasu shi ne duba shirye-shiryen karbar dan takararsu na shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar.

  • 2023: Hotunan Atiku Sun Yi Batan-Dabo A Motocin Yakin Neman Zaben PDP A Jihar Ribas

Barista Kabiru Turaki, wanda tsohon ministan ayyuka na musamman ne, ya ce makasudin taron shi ne duba shirye-shiryen karbar dan takararsu na shugaban kasa.

Ya ce: “Abin da za a yi a yau shi ne duba shirye-shiryen karbar dan takararmu na shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar, GCON, Wazirin Adamawa, wanda ake sa ran zai ziyarce mu a nan Kebbi a ranar Asabar 12 ga watan Nuwamba, 2022 don gudanar da yakin neman zaben shugaban kasa ga al’ummar jihar.

Haka kuma, Barista Turaki ya tunatar da cewa ziyarar da Atiku ya kai jihar Kebbi a shekarar 2019 ita ce mafi kyau da aka taba samu a kasar nan, yayin da ya kuma ba da tabbacin jam’iyyar ta kuduri aniyar yiwa maziyartan liyafar da ta dace fiye da ziyarar da ya kawo a baya.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Don haka kudurinmu a yau shi ne mu ma mu rubanya adadin mutane, mun zauna mun kafa kwamitocin da za su yi aiki awa 24 daga yanzu har zuwan sa da kuma tafiyarsa a ranakun 12 da 13 ga Nuwamba, 2022.

“Daga nan za mu ziyarci filin wasa na Birnin Kebbi domin duba irin ayyukan da ake yi a can.

“Don haka muna so mu tabbatar wa ‘yan Nijeriya da mambobin kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa cewa shugabancin jam’iyyar PDP a jihar Kebbi a shirye yake ya karbi dan takararta na shugaban kasa,, a Jihar kebbi, in ji shi”.

Daga karshe, Barista Kabiru Turaki SAN, ya lissafa kwamitocin da suka hada da; babban kwamitin da tsohon Janar Ishaya Bamaiyi zai jagoranta, kwamitin wurin, kwamitin tsaro, kwamitin masauki, kwamitin sufuri, kwamitin nishaɗi da kwamitin yada labarai.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
Siyasa

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
Xi Jinping Jagoran Sabon Tafarki

Xi Jinping Jagoran Sabon Tafarki

LABARAI MASU NASABA

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.