• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyar PDP A Kebbi Ta Shirya Tarbar Dan Takarar Shugaban Kasa, Atiku Abubakar

by Sulaiman and Umar Faruk
3 years ago
in Siyasa
0
Jam’iyyar PDP A Kebbi Ta Shirya Tarbar Dan Takarar Shugaban Kasa, Atiku Abubakar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PDP reshen jihar Kebbi ta bayyana cewa ta shirya tsaf domin tarbar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Atiku Abubakar, GCON, a ranar 12 ga watan Nuwamba a jihar.

Da yake jawabi ga manema labarai a Birnin Kebbi, babban birnin jihar, Barista Kabiru Tanimu Turaki SAN, mamba a kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP (BOT) ya ce makasudin taron nasu shi ne duba shirye-shiryen karbar dan takararsu na shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar.

  • 2023: Hotunan Atiku Sun Yi Batan-Dabo A Motocin Yakin Neman Zaben PDP A Jihar Ribas

Barista Kabiru Turaki, wanda tsohon ministan ayyuka na musamman ne, ya ce makasudin taron shi ne duba shirye-shiryen karbar dan takararsu na shugaban kasa.

Ya ce: “Abin da za a yi a yau shi ne duba shirye-shiryen karbar dan takararmu na shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar, GCON, Wazirin Adamawa, wanda ake sa ran zai ziyarce mu a nan Kebbi a ranar Asabar 12 ga watan Nuwamba, 2022 don gudanar da yakin neman zaben shugaban kasa ga al’ummar jihar.

Haka kuma, Barista Turaki ya tunatar da cewa ziyarar da Atiku ya kai jihar Kebbi a shekarar 2019 ita ce mafi kyau da aka taba samu a kasar nan, yayin da ya kuma ba da tabbacin jam’iyyar ta kuduri aniyar yiwa maziyartan liyafar da ta dace fiye da ziyarar da ya kawo a baya.

Labarai Masu Nasaba

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

“Don haka kudurinmu a yau shi ne mu ma mu rubanya adadin mutane, mun zauna mun kafa kwamitocin da za su yi aiki awa 24 daga yanzu har zuwan sa da kuma tafiyarsa a ranakun 12 da 13 ga Nuwamba, 2022.

“Daga nan za mu ziyarci filin wasa na Birnin Kebbi domin duba irin ayyukan da ake yi a can.

“Don haka muna so mu tabbatar wa ‘yan Nijeriya da mambobin kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa cewa shugabancin jam’iyyar PDP a jihar Kebbi a shirye yake ya karbi dan takararta na shugaban kasa,, a Jihar kebbi, in ji shi”.

Daga karshe, Barista Kabiru Turaki SAN, ya lissafa kwamitocin da suka hada da; babban kwamitin da tsohon Janar Ishaya Bamaiyi zai jagoranta, kwamitin wurin, kwamitin tsaro, kwamitin masauki, kwamitin sufuri, kwamitin nishaɗi da kwamitin yada labarai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kudin Shigar Kamfanonin Gwamnatin Sin A Rubu’i Uku Na Farkon Bana Ya Karu Da Kaso 10.9 Bisa Dari

Next Post

Xi Jinping Jagoran Sabon Tafarki

Related

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta
Siyasa

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

14 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

17 hours ago
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson
Siyasa

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

21 hours ago
Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP
Manyan Labarai

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

3 days ago
Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

4 days ago
An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027
Siyasa

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

5 days ago
Next Post
Xi Jinping Jagoran Sabon Tafarki

Xi Jinping Jagoran Sabon Tafarki

LABARAI MASU NASABA

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.