• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jerin Kasashen Da Ke Fama Da Tsananin Zafin Da Ba A Taba Yi Ba

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Kasashen Ketare
0
Jerin Kasashen Da Ke Fama Da Tsananin Zafin Da Ba A Taba Yi Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasashe da dama na duniya na ci gaba da fama da tsananin zafi mai hadarin gaske, inda hukumomi ke ba jama’a shawarwari kan irin matakan da za su dauka na kare kai da sauran masu rauni daga illar yanayin.

A wasu kasashen ma ta kai ga ana kwashe mutane daga yankunansu saboda illar gobarar daji, wadda yanayin zafin ke haddasawa.

  • Sin Da Amurka Sun Gudanar Da Taron Tattaunawa Kan Sauyin Yanayi a Birnin Beijing

Tuni kasashe da dama musamman wadanda suke bangaren Arewacin duniya suke fama da wannan matsala ta tsananin zafi da kusan ba a taba ganin irinta ba a baya.

Kasashen su ne na nahiyar Amurka ta Arewa da Turai da yawancin kasashen Asiya da wasu kasashen Arewa maso Kudancin Latin Amurka da kuma Arewacin Afirka.

Kasashen da ke yankin tekun Bahar-Rum na daga cikin wadanda suka fi dandana kudarsu a wannan sauyi na zafi da ake gani.

Labarai Masu Nasaba

Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah

Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa

Tsawon kwanaki kasashen Italiya da Sifaniya da Girka suke fama da tsananin zafin.
Ma’aikatar lafiya ta Italiya ta yi gargadi da ankarar da jama’a game da illoli da matakan da ya kamata su dauka, domin kariya, a biranen kasar 16, wadanda suka hada da babban birni, Rum da Bologna da Florence.

Kuma hukumomin kasar suna ganin matsalar za ta ci gaba har wannan satin da za a shiga, inda yanayin zafin zai iya kai wa maki 48 a ma’aunin Selshiyas a birnin Sardinia, kamar yadda aka ruwaito a kafafen yada labaran kasar ta Italiya.

Haka kuma ake ganin lamarin zai kasance a sauran sassan Kudancin Turai.
Masanin kimiyyar suffa, kuma tsohon ministan makamashi na Italiya Roberto Cingolani ya gaya wa BBC cewa halin da ke ciki ya sa mutane sun fara fahimtar alakar tsananin sauyin yanayin da ke faruwa da kuma dumamar yanayi a duniya;
Ya ce, tsawon shekaru ana raina matsalar sauyin yanayi da dumamar yanayi, yanzu mun makara.

Ina ganin yawancin gwamnatoci a yanzu suna aiki sosai su rage tasirin sauyin yanayi.
To amma tun da wannan kamar wani yanayi ne ake na gaggawa, sai ya kasance muna ta fama da shi kawai.

Masanin ya kara da cewa, ba ruwan yanayi na duniya da siyasa da wata yarjejeniya da kuma kutungwilar mutane. Ita duniya tana gudana ne yadda take a tsare.

‘’Kuma ina ganin yanzu mun yarda ba wani kokwanto cewa abubuwa na sauyawa, wanda dole kowa ya tashi tsaye ya yi wani abu’’ in ji shi.

Ya kara da cewa ; ‘’A don haka ina ganin watakila duniya za ta koya mana darasi dukkaninmu cewa sai mun kara himma.’’
Haka ake ganin tsananin zafin zai ci gaba ya kai matakin da ba a taba kaiwa ba a sauran sassan Turan ba tare da ganin alamar sauki ba a cikin makon mai shigowa.

A Sifaniya zafin ya haddasa gobarar daji a tsibirin La Palma, da ke kusa da gabar tekun Afirka, inda aka kwashe akalla mutum dubu biyu 2000, yayin da wutar ke ci ganga-ganga.
Ita ma Moroko a bangaren Afirka na wannan yanki na tekun Bahar-Rum ta shiga rukunin da hukumomi ke yi wa jama’a gargadi a kan tsananin zafin.

Haka ita ma Amurka, wadda kashi daya bisa uku na al’ummarta ke cikin tsananin zafin, can a yankinta na Kudu maso Yamma ana fama da zafin sosai, inda a birnin Phoenid, zafin ya wuce maki 43 a ma’aunin Selshiyas, sama da mako biyu.

Hukumomi na gargadin mutane da cewa duk wanda ba shi da wani tanadi kyakkyawa na na’urar sanyaya muhallinsa ko wadata kai da isasshen ruwa to fa yana cikin hadari.

Jamus, ma abin mamaki ba ta tsira daga matsalar ba ta tsananin zafi, inda ‘yan siyasa suka bi sahu na gargadin cewa bala’in sauyin yanayi tuni ya fara hallaka jama’a.

Wasu sassan kasar China da Japan su ma ba su tsira ba daga yanayin na tsananin zafin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Diphtheria: Mutum 3 Sun Rasu, An Kwantar Da 7 A Asibiti A Kaduna

Next Post

Kungiyar Ma’aikatan AKTH Na Da Burin Kafa Bankin Kanta – Abba Yakasai

Related

Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah

23 hours ago
Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa
Kasashen Ketare

Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa

2 days ago
Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini
Kasashen Ketare

Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini

3 days ago
Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon
Kasashen Ketare

Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon

6 days ago
Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
Ilimi

Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China

1 week ago
Gwamnatin Trump Na Shirin Rufe Ofisoshin Jakadanci A Afrika
Kasashen Ketare

Gwamnatin Trump Na Shirin Rufe Ofisoshin Jakadanci A Afrika

3 weeks ago
Next Post
Kungiyar Ma’aikatan AKTH Na Da Burin Kafa Bankin Kanta – Abba Yakasai

Kungiyar Ma’aikatan AKTH Na Da Burin Kafa Bankin Kanta - Abba Yakasai

LABARAI MASU NASABA

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.