ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jerin Kasashen Da Ke Fama Da Tsananin Zafin Da Ba A Taba Yi Ba

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Zafi

Kasashe da dama na duniya na ci gaba da fama da tsananin zafi mai hadarin gaske, inda hukumomi ke ba jama’a shawarwari kan irin matakan da za su dauka na kare kai da sauran masu rauni daga illar yanayin.

A wasu kasashen ma ta kai ga ana kwashe mutane daga yankunansu saboda illar gobarar daji, wadda yanayin zafin ke haddasawa.

  • Sin Da Amurka Sun Gudanar Da Taron Tattaunawa Kan Sauyin Yanayi a Birnin Beijing

Tuni kasashe da dama musamman wadanda suke bangaren Arewacin duniya suke fama da wannan matsala ta tsananin zafi da kusan ba a taba ganin irinta ba a baya.

ADVERTISEMENT

Kasashen su ne na nahiyar Amurka ta Arewa da Turai da yawancin kasashen Asiya da wasu kasashen Arewa maso Kudancin Latin Amurka da kuma Arewacin Afirka.

Kasashen da ke yankin tekun Bahar-Rum na daga cikin wadanda suka fi dandana kudarsu a wannan sauyi na zafi da ake gani.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Tsawon kwanaki kasashen Italiya da Sifaniya da Girka suke fama da tsananin zafin.
Ma’aikatar lafiya ta Italiya ta yi gargadi da ankarar da jama’a game da illoli da matakan da ya kamata su dauka, domin kariya, a biranen kasar 16, wadanda suka hada da babban birni, Rum da Bologna da Florence.

Kuma hukumomin kasar suna ganin matsalar za ta ci gaba har wannan satin da za a shiga, inda yanayin zafin zai iya kai wa maki 48 a ma’aunin Selshiyas a birnin Sardinia, kamar yadda aka ruwaito a kafafen yada labaran kasar ta Italiya.

Haka kuma ake ganin lamarin zai kasance a sauran sassan Kudancin Turai.
Masanin kimiyyar suffa, kuma tsohon ministan makamashi na Italiya Roberto Cingolani ya gaya wa BBC cewa halin da ke ciki ya sa mutane sun fara fahimtar alakar tsananin sauyin yanayin da ke faruwa da kuma dumamar yanayi a duniya;
Ya ce, tsawon shekaru ana raina matsalar sauyin yanayi da dumamar yanayi, yanzu mun makara.

Ina ganin yawancin gwamnatoci a yanzu suna aiki sosai su rage tasirin sauyin yanayi.
To amma tun da wannan kamar wani yanayi ne ake na gaggawa, sai ya kasance muna ta fama da shi kawai.

Masanin ya kara da cewa, ba ruwan yanayi na duniya da siyasa da wata yarjejeniya da kuma kutungwilar mutane. Ita duniya tana gudana ne yadda take a tsare.

‘’Kuma ina ganin yanzu mun yarda ba wani kokwanto cewa abubuwa na sauyawa, wanda dole kowa ya tashi tsaye ya yi wani abu’’ in ji shi.

Ya kara da cewa ; ‘’A don haka ina ganin watakila duniya za ta koya mana darasi dukkaninmu cewa sai mun kara himma.’’
Haka ake ganin tsananin zafin zai ci gaba ya kai matakin da ba a taba kaiwa ba a sauran sassan Turan ba tare da ganin alamar sauki ba a cikin makon mai shigowa.

A Sifaniya zafin ya haddasa gobarar daji a tsibirin La Palma, da ke kusa da gabar tekun Afirka, inda aka kwashe akalla mutum dubu biyu 2000, yayin da wutar ke ci ganga-ganga.
Ita ma Moroko a bangaren Afirka na wannan yanki na tekun Bahar-Rum ta shiga rukunin da hukumomi ke yi wa jama’a gargadi a kan tsananin zafin.

Haka ita ma Amurka, wadda kashi daya bisa uku na al’ummarta ke cikin tsananin zafin, can a yankinta na Kudu maso Yamma ana fama da zafin sosai, inda a birnin Phoenid, zafin ya wuce maki 43 a ma’aunin Selshiyas, sama da mako biyu.

Hukumomi na gargadin mutane da cewa duk wanda ba shi da wani tanadi kyakkyawa na na’urar sanyaya muhallinsa ko wadata kai da isasshen ruwa to fa yana cikin hadari.

Jamus, ma abin mamaki ba ta tsira daga matsalar ba ta tsananin zafi, inda ‘yan siyasa suka bi sahu na gargadin cewa bala’in sauyin yanayi tuni ya fara hallaka jama’a.

Wasu sassan kasar China da Japan su ma ba su tsira ba daga yanayin na tsananin zafin.

Zafi
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Kasashen Ketare

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
Kasashen Ketare

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

July 5, 2026
Next Post
Kungiyar Ma’aikatan AKTH Na Da Burin Kafa Bankin Kanta – Abba Yakasai

Kungiyar Ma’aikatan AKTH Na Da Burin Kafa Bankin Kanta - Abba Yakasai

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.