• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jerin Manyan Jaruman Fim Da Nijeriya Ta Rasa A Yan Shekarun Nan

by Rabilu Sanusi Bena
4 weeks ago
in Nishadi
0
Jerin Manyan Jaruman Fim Da Nijeriya Ta Rasa A Yan Shekarun Nan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masana’antar shirya fina-finan Nijeriya ta yi shura wajen shirya manyan fina finai masu nishadantarwa, fadakarwa da kuma wa’azantarwa, fina finan kudancin Nijeriya sun fara ne daga karamar masana’anta har ta kai ga zama babbar cibiyar duniya da muka sani a yau a matsayin Nollywood, hakazalika Kannywood wadda ta kasance gishiri cikin miyar masana’antar nishadi da al’adu ta nahiyar Afirika a halin yanzu. 

Yayin da masana’antar ke ci gaba da fitar da sabbin jarumai masu hazaka da suka kafa tarihin zama wani madubi ga yara masu tasowa, har yanzu tabon rashin wasu fitattun fuskoki bai gushe daga zuciyar babbar masana’antar ta nishadi ba, a wani yanayi da za a iya kira na juyayi jaruman sun wuce sun bar wani wagegen gibi wanda ba lallai bane a samu wani jarumi da zai iya cikawa ba.

  • Kwararru Sun Yi Musayar Ra’ayoyi Dangane Da Wayewar Kan Sin Da Afirka 
  • Fursunoni 62 Sun Rubuta Jarrabawar NECO da MBAIS A Kano

A wannan mako LEADERSHIP Hausa ta zakulo wasu fitattun fuskokin jaruman manyan masana’antun nishadi na Nollywood da Kannywood da su ka kwanta dama, da ba za a taba iya mantawa da gudunmawar da su ka bayar ga masana’antar ba.

 

1. Sam Loco Efe

Labarai Masu Nasaba

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

Fitaccen jarumi Sam Loco Efe jarumin barkwanci ne a Nijeriya da aka haifa ranar 25 ga watan Disamba a shekarar 1945, a Jihar Enugu, ya girma a Abakaliki, Jihar Ebonyi, tarihin Sam a wasan kwaikwayo ya fara ne a cikin wasan kwaikwayon “Langbodo” a lokacin FESTAC ’77, inda a nan ne aka gane irin tarin baiwar da yake da ita a bangaren wasan kwaikwayo, Loco ya saka sunashi a cikin jerin sunayen fitattun ‘yan wasan Afirka.

Loco ya shafe tsawon lokaci a wannan bangaren da kuma wasannin talabijin kamar “Hotel de Jordan” da kuma fina-finan Nollywood da yawa, kwarewarshi a harshen Ingilishi ya sa galibi yake isar da sakonni masu rikitarwa ga masu kallo ba tare da wahala ba, masu sharhi sun taba bayyana shi a matsayin “Dan wasan Nollywood mafi hazaka da ya taba rayuwa a Duniya, Sam Loco Efe ya rasu ne a ranar 7 ga Agusta, 2011, yana da shekaru 65 a duniya.

 

2. Rabilu Musa (Ibro)

Rabilu Musa wanda aka fi sani da Dan Ibro, fitaccen jarumin barkwanci ne kuma jarumi a masana’antar fina-finan Kannywood, an haife shi a ranar 12 ga Disamba, 1971, a garin Danlasan na jihar Kano, ya fara karatunsa a makarantar firamare ta Danlasan, daga nan kuma ya halarci Kwalejin Malamai ta Gwamnati da ke Wudil, a shekarar 1991, ya shiga aikin kula da gidajen yari na Nijeriya, inda ya yi aiki kafin ya fara wasannin barkwanci.

Fim din Dan Ibro na farko mai suna “Yar Mai Ganye” ya nuna yadda Ibro ya yi fice a fagen barkwanci, salon sa na musamman da barkwancinsa ya na burge masu kallo, wanda hakan ya sa ya yi suna a arewacin Nijeriya, a tsawon shekaru, ya fito a fina-finai da dama, da suka hada da “Ibro Dan Almajiri”, “Ibro Police”, da “Ibro Dan Fulani”.

A tsawon rayuwarsa, Dan Ibro ya samu yabo da dama saboda gudunmawar da ya bayar a harkar fim, musamman ma, an karrama shi da lambar yabo ta Best Comedian award a Kannywood Awards 2015, Rabilu Musa ya rasu ne a ranar 9 ga watan Disamba, 2014, yan kwanaki kadan ya cika cika shekaru 43 a duniya, mutuwar sa ta bar gibi sosai a Kannywood.

 

3. Justus Esiri

Justus Esiri fitaccen dan wasan Nijeriya ne, an haife shi a ranar 20 ga Nuwamba, 1942, a Oria-Abraka, jihar Delta, ya halarci kwalejin Urhobo da ke Effurun kafin ya koma Jamus don ci gaba da karatu, a can ya yi karatu a cibiyoyi daban daban, ciki har da Jami’ar Madimilian a Munich inda ya kamu da sha’awar wasan kwaikwayo, Justua ya fara harkar wasan kwaikwayo a Jamus, inda ya yi wasa a tsakanin 1968 zuwa 1969.

Da ya dawo Nijeriya, Justus ya yi suna saboda rawar da ya taka a cikin fitaccen shirin talabijin mai suna “The Billage Headmaster”, inda ya fito a matsayin shugaban makaranta, a tsawon shekarun aikinsa, ya fito a cikin fina-finai da shirye-shiryen Talabijin da dama, ciki har da “Wasted Years”, “Foreber”, da “Coridors of Power”, ya sami lambobin yabo da yawa, ciki har da kyautar mafi kyawun jarumi a bikin karramawa ta 9th Africa Mobie Academy Awards saboda rawar da ya taka a “Assassins Practice”, Gwamnatin Nijeriya ta kuma karrama shi da mukamin Officer of the Order of the Niger (OON), Justus Esiri ya rasu ne a ranar 19 ga Fabrairu, 2013, a Legas bayan fama da cutar ciwon suga.

 

4. Hajiya Zainab Booth

Hajiya Zainab Musa Booth ta kasance fitacciyar jaruma a masana’antar shirya fina-finan Kannywood, an haife ta a shekarar 1960, mahaifiyarta Bafulatana inda kuma mahaifinta ya kasance dan kasar Scotland, wannan ya matukar taimakawa basirar da Zainab takeda ita a harkar fim ta hanyar nuna mabanbantan al’adu da zamantakewa da ta koya a wajen iyayenta da suke a mabanbantan kabilu, wanda hakan ya sa mafi yawancin masu kallo a duk fadin arewacin Nijeriya ke son ta.

Bayan aikin wasan kwaikwayo, Zainab ta kasance uwa ga ‘ya’ya hudu, ciki har da fitattun jaruman Kannywood Maryam Booth da Amude Booth, Zainab Booth ta rasu ne a ranar 1 ga Yuli, 2021, tana da shekaru 61, bayan gajeruwar rashin lafiya inda aka yi jana’iizarta a birnin Kano, Al’ummar Kannywood sun yi alhinin rasuwar ta.

 

5. Bukky Ajayi

An haifi Bukky Ajayi a ranar 2 ga watan Fabrairu, 1934, ta yi karatun sakandare a Ingila inda ta samu tallafin karatu na gwamnatin tarayya, bayan ta yi shekaru shida a kasar waje, ta dawo Nijeriya a shekarar 1965, ta fara aikin gabatar da shirye-shirye da labarai a gidan talabijin na Nijeriya (NTA) a shekarar 1966.

Tarihin wasan kwaikwayon Bukky ya fara ne da shirin talabijin na “Billage Headmaster” a cikin shekarun 1970, wanda ya sa ta zama sananniya a yawancin gidajen Nijeriya, a tsawon rayuwarta ta fito a cikin fina-finai da yawa, ciki har da “Diamond Ring”, “Witches”, da “Thunderbolt”, don karrama gagarumar gudunmawar da ta bayar a Nollywood, Bukky ta sami lambar yabo ta Africa Magic Biewers Choice Awards a shekarar 2016, Bukky Ajayi ta rasu a ranar 6 ga Yuli 2016, tana da shekaru 82 a duniya.

 

6. Saratu Gidado

Ita dai Saratu Gidado, an haife ta a Jihar Gombe, a ranar 17 ga watan Janairu 1968, ta yi karatu tun daga matakin firamare a Jihar Kano, Daso, wadda tayi suna wajen fitowa a matsayin “Ba Sani Ba Sabo” a shirye shiryenta, ta kasance abar so a wajen masu kallo saboda yadda take yin abu da gaske kuma babu tsoro a cikin Shirin Fim, Daso ta yi suna ne musamman wajen fitowa a matsayin mara tsoro kuma masifaffiya, hakan ya sa ta fita daban a cikin ragowar jarumai mata a masana’antar saboda ta na iya fitowa a duk yanayin da ake bukata ta fito musamman a matsayin uwa mai tsoratarwa.

A shekara ta 2000 ta tsunduma harkokin fina finan hausa, inda ta fara fitowa a cikin Shirin “Linzami Da Wuta” wanda kamfanin Sarauniya ya shirya, wasu daga cikin fina finan da ta fito sun hada da “Yar Mai Ganye”, “Nagari”, “Fil’azal” da kuma Shirin turanci na “There is Way” da kamfanin Jammaje ya shirya, a shekarar 2016 ne Sarkin Kano na 14 Muhammad Sanusi II ya nada ta a matsayin Jakadiya, kamar yadda iyalai da yan uwanta suka bayyana, ta rasu da safiyar Talata 9 ga watan Afrilu na shekarar 2024.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FinafinaiJarumaiRasuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 15 Na Birnin Beijing

Next Post

Wang Yi Ya Yi Bayani Kan Ziyarar Shugaba Xi Jinping A Vietnam Da Malaysia Da Cambodia

Related

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

4 days ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

4 days ago
Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe
Nishadi

Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe

2 weeks ago
Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje
Nishadi

Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje

3 weeks ago
Daga Kaina An Gama Harkar Fim A Zuri’ata – Moda
Nishadi

Daga Kaina An Gama Harkar Fim A Zuri’ata – Moda

3 weeks ago
Rarara Zai Angwance Da Aisha Humaira Yau A Maiduguri
Manyan Labarai

Rarara Zai Angwance Da Aisha Humaira Yau A Maiduguri

3 weeks ago
Next Post
Wang Yi Ya Yi Bayani Kan Ziyarar Shugaba Xi Jinping A Vietnam Da Malaysia Da Cambodia

Wang Yi Ya Yi Bayani Kan Ziyarar Shugaba Xi Jinping A Vietnam Da Malaysia Da Cambodia

LABARAI MASU NASABA

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.