• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Bauchi Ta Lashe Lambar Yabon Kwazo A Bangaren Mai Da Iskar Gas

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Jihar Bauchi Ta Lashe Lambar Yabon Kwazo A Bangaren Mai Da Iskar Gas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamfanin Rana Continental Synergy da hadin guiwar gwamnatin tarayya, sun karrama jihar Bauchi a matsayin gwarzowar jiha mai tasowa a bangaren mai da iskar gas ta shekarar 2024.

Gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad ne ya amshi lambar yabon a madadin jihar, a yayin babban taron liyafa ta bangaren iskar gas da mai na Nijeriya da ya gudana a Abuja, wanda kuma kamfanin Rana Continental Syngergy ta shirya da hadin guiwar masu ruwa da tsaki a bangaren mai da iskar gas hadi da ma’aikatar albarkatun mai.

  • Samar Da Jami’ar Musulunci A Jihar Kaduna Alheri Ne – Bola Ige
  • Xi Ya Mika Gaisuwar Bikin Bazara Ga Dukkan Sinawa

Bala Muhammad wanda ya jinjina da kokarin masu shirya taron wajen zabar jihar gami da karramata, ya sha alwashin hada kai da shugaban kasa Bola Tinubu domin cimma manufar gwamnatin tarayya na shawo kan matsalolin da suka yi wa bangaren tattalin arzikin kasa dabaibayi.

Da ya ke samun wakilcin kwamishinan albarkatun kasa na jihar Bauchi, Hon. Muhammad Maiwada Bello, gwamnan ya misalta taron a matsayin mai cike da tarihi ta yadda jihar ta lashe kambon jiha mai tasowa a bangaren mai da iskar gas a 2024 a fadin kasar nan.

Ya ce, wannan nasarar da jihar ta samu bai rasa nasaba da tsare-tsare da kyawawan manufofin da suke akwai a bangaren mai da gas gami da saukaka harkokin kasuwanci musamman bayan gano Mai a kogin Kolmani da ke karamar hukumar Alkaleri a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

Ya ce, hakan zai kara janyo hankalin masu sha’awar zuba hannun jari domin su zo jihar su zuba hannun jarinsu domin cigaban jihar da ma kasa baki daya.

Maiwada Bello, ya ce, gwamnan jihar Bauchi na aiki tukuru domin kyautata bangaren makamashi domin tabbatar da samar da damarmakin zuba jari da ayyukan yi ga matasa.

Ya kuma ce, lambar yabon zai kara musu kumaji da kokarin zage damtse wajen yin duk mai yiyuwa domin kunkasa bangarorin makamashi.

A nasa jawabin, karamin minista (Gas) a ma’aikatar albarkatun mai, Ekperikpe Ekpo, ya ce, jihar Bauchi ta nuna kwarin guiwar za ta yi abun a zo a gani a bangaren makamashi yayin da take kokarin samar da damarmaki da kere-kere a bangaren masana’antun mai da gas a Nijeriya.

Da ya ke samun wakilcin daraktan gas na ma’aikatar Misis Oluremi Komolafe, ta ce, lambar yabon ya cancanci jihar Bauchi lura da rawar da take takawa wajen kyautata harkokin mai da iskar gas.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci gaban TechnologyJihar BauchiTattalin Arziki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Karancin Gas Ya Jefa Al’umma Cikin Duhu Da Matsaloli A Bangaren Lantarki A Nijeriya

Next Post

Sojojin Sama Ga INEC: Ku Biya Mu Bashi Don Mu Ji Dadin Aiki Tukuru

Related

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno
Labarai

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

51 minutes ago
Labarai

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

4 hours ago
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai
Manyan Labarai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

4 hours ago
Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya
Labarai

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

7 hours ago
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
Labarai

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

16 hours ago
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara
Labarai

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

17 hours ago
Next Post
Sojojin Sama Ga INEC: Ku Biya Mu Bashi Don Mu Ji Dadin Aiki Tukuru

Sojojin Sama Ga INEC: Ku Biya Mu Bashi Don Mu Ji Dadin Aiki Tukuru

LABARAI MASU NASABA

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

September 6, 2025
Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

September 6, 2025
Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.