ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Katsina Ta Kafa Kwamitin Rabon Shinkafar Da Tinubu Ya Bayar

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Katsina

Gwamnatin Jihar Katsina ta kafa kwamiti don rarraba shinkafar da gwamnatin tarayya ta bayar. Wannan sanarwa ta fito ne daga Kwamishinan yaɗa labarai da Al’adu, Dr. Bala Salisu-Zango, a ranar Litinin a Katsina. Mukaddashin Gwamna Malam Faruk Lawal-Jobe ya naɗa Sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Abdullahi Garba-Faskari, a matsayin shugaban kwamitin.

Sauran membobin kwamitin sun haɗa da Mashawarci na Musamman kan Ayyukan Jama’a, Kwamishinonin Ayyuka na Musamman, da wakilin Majalisar Dokokin Jiha, da kuma wasu jami’an ƙananan hukumomi da wakilan hukumomin tsaro, da kungiyoyin addini, da ƙungiyoyin matasa, da kuam ƙungiyoyin farar hula.

  • Gwamna Radda Ya Amince Da Bai Wa Ma’aikata N15,000 A Matsayin Goron Sallah
  • Katsina United Ta Kammala Ɗaukar Ƴan Wasa Biyu Daga Kano Pillars 

Kwamitin zai tabbatar da adadin buhunan shinkafar da aka karɓa daga Gwamnatin Tarayya da kuma tsara yadda za a rarraba shinkafar a fadin ƙananan hukumomi 34 na jihar. Ayyukan su sun haɗa da tabbatar da tsarin rarraba shinkafar cikin gaskiya da adalci, musamman ga marasa galihu kamar gwauraye, zawarawa, da tsofaffi maza da mata.

ADVERTISEMENT

Dr. Salisu-Zango ya jaddada muhimmancin waɗannan matakai don tabbatar da adalci wajen rarraba kayan ga waɗanda suke da buƙata.

Dr. Salisu-Zango ya kuma bayyana cewa ana sa ran kwamitin zai miƙa rahotonsa cikin makonni uku.

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Mukaddashin gwamnan ya tabbatar da cewa jihar ta karɓi manyan motocin shinkafa guda 20 daga gwamnatin tarayya, kuma gwamnatin jiha ta samar da tallafin jigilar kayayyakin don sauƙaƙe rarrabawa zuwa wurare daban-daban a cikin ƙananan hukumomi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Next Post
Sakamakon Zanga-Zanga MTN Ta Rufe Ofisoshinta Na Kasar Gaba Ɗaya 

Sakamakon Zanga-Zanga MTN Ta Rufe Ofisoshinta Na Kasar Gaba Ɗaya 

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.