• English
  • Business News
Monday, September 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Kogi Ta Kulla Yarjejeniyar Bunkasa Noma Da Kungiyar Solidaridad

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Jihar Kogi Ta Kulla Yarjejeniyar Bunkasa Noma Da Kungiyar Solidaridad
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kogi ta kulla yarjeniya da kungiyar aikin noma ta kasa da kasa (Solidaridad), don kara bunkasa fannin aikin noma da kuma kara samar da wadataccen abinci a jihar da ma kasa baki-daya.

Gwamnan Jihar, Ahmed Usman Ododo ne ya bayyana haka a lokacin kaddamar da aikin noma kashi na biyu da aka gudanar a babban birnin tarrayya Abuja.

  • Kasar Philippines Na Kara Hauka Kan Batun Tekun Kudancin Kasar Sin
  • Shettima Ya Ƙaddamar Da Ginin Ofishin Hukumar Raya Arewa Maso Gabas

Ododo ya bayyana hakan ne ta bakin Sakatariyar Gwamnatin Jihar, Dakta Folashade Arike Ayoade.

Har ila yau, ya bayyana cewa; gwamnatin tasa ta sha alwashin inganta

aikin noma a jihar, musamman duba da ganin yadda ta mallaki babbar gonar da ke garin Suleja a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

A cewar tata, Allah ya albarkaci jihar da dimbin damammaki a wannan bangare na aikin noma tare kuma da ingantacciyar kasar noman.

Har ila yau kuma, ta yaba wa kungiyar ta Solidaridad da kuma NIPCONS, bisa tunawa da jihar ta Kogi a bangaren aikin noma da suka yi.

Folashade ta kuma bayar da tabbacin mayar da hankalin gwamnatin jihar, wajen kara habaka fannin aikin noma a fadin jihar baki-daya.

Haka zalika, ta yaba wa Gwamnatocin Kasar Amurka da Netherlands; kan yin hadaka a kan shirin na habaka aikin noma na jihar.

Ta kara da cewa, babu shakka al’ummar jihar da dama sun amfana da ayyukan wannan kungiya ta NISCOPS.

Ta ci gaba da cewa, bisa kaddamar da kashi na biyu na kungiyar NISCOPS a jihar, sannan Gwamnatin Jihar Kogi a shiye take wajen yin hadaka da kunyoyin Solidaridad da kuma IDH, domin amfana da karin wasu shiye-shiryensu, musamman don samar da sakamako mai matukar kyau.

“Bisa rattaba hannun yarjejeniyar da kananan hukumomi uku suka yi da wannan kungiya ta Solidaridad, kan shirin masu ruwa da tsaki na noman Kwakwar Manja na kasa (NISCOPS), hakan zai bai wa Jihar Kogi damar mayar da hankali, musamman a kan wannan fanni na noma; don samun gwaggwabar riba.

Folashade ta ci gaba da cewa, “Gwamnatin Kogi ta gode wa Gwamnatocin Kasashen Netherlands da kuma Ingila, kan dabbaka wannan shiri, musamman domin yaki da kalubalen sauyin yanayi, wanda hakan zai kara taimakawa wajen kara samar da wadataccen abinci; ba a jihar kadai ba, har da ma fadin kasa baki-daya.

Shi kuwa shugaban hukumar, Daan Wensing ya sanar da cewa; ana samun karin bukatar Manja, musamman saboda amfanin da yake da shi da kuma neman sa da ake yi a daukacin fadin duniya baki-daya.

Har wa yau kuma ya bayyana cewa, a karkashin shirin hadakar na NISCOPS da Solidariadad, kananan manoma ake bukata su amfana da shirin, ba wadanda suka ci suka tayar da kai ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KogiKulla Yarjejeniya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Firaministan Djibouti Ya Baiwa Rukunin Tallafin Jinya Na Kasar Sin Karo Na 22 Lambar Yabo

Next Post

Ministan Niger: Kullum Niger Tana Daukar Sin a Matsayin Abokiyar Hadin Kanta Ta Farko

Related

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

1 week ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

1 week ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

2 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

2 weeks ago
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

3 weeks ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

3 weeks ago
Next Post
Ministan Niger: Kullum Niger Tana Daukar Sin a Matsayin Abokiyar Hadin Kanta Ta Farko

Ministan Niger: Kullum Niger Tana Daukar Sin a Matsayin Abokiyar Hadin Kanta Ta Farko

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Gana Da Narendra Modi 

Xi Jinping Ya Gana Da Narendra Modi 

August 31, 2025
Xi Jinping Da Uwargidansa Peng Liyuan Sun Shirya Liyafar Maraba Da Baki Na Kasa Da Kasa Ga Mahalarta Taron SCO

Xi Jinping Da Uwargidansa Peng Liyuan Sun Shirya Liyafar Maraba Da Baki Na Kasa Da Kasa Ga Mahalarta Taron SCO

August 31, 2025
Gobarar Tankar Mai Ta Lakume Manyan Motoci 4 A Legas

Gobarar Tankar Mai Ta Lakume Manyan Motoci 4 A Legas

August 31, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Farfado Da Kasa Bisa Karfin Ruhin Turjiya Ga Zalunci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Farfado Da Kasa Bisa Karfin Ruhin Turjiya Ga Zalunci

August 31, 2025
Kano Na Asarar Biliyan 1 Duk Shekara Dalilin Rashin Yin Gwanjon Tsofaffin Kayan

Kano Na Asarar Biliyan 1 Duk Shekara Dalilin Rashin Yin Gwanjon Tsofaffin Kayan

August 31, 2025
Kasar Sin Ta Inganta Wuraren Tunawa Da Tarihi Don Bikin Samun Nasara Kan Zaluncin Japanawa

Kasar Sin Ta Inganta Wuraren Tunawa Da Tarihi Don Bikin Samun Nasara Kan Zaluncin Japanawa

August 31, 2025
Jami’an Senegal Sun Yaba Da Ci Gaban Da Aka Samu Wajen Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing

Jami’an Senegal Sun Yaba Da Ci Gaban Da Aka Samu Wajen Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing

August 31, 2025
Ɗan Majalisa Zai Saya Wa Makinde Fam Ɗin Takarar Shugaban Ƙasa A 2027

Ɗan Majalisa Zai Saya Wa Makinde Fam Ɗin Takarar Shugaban Ƙasa A 2027

August 31, 2025
Fim Din Kasar Sin Kan Kisan Kiyashin Nanjing Ya Ja Hankulan Masu Kallo A Nijeriya

Fim Din Kasar Sin Kan Kisan Kiyashin Nanjing Ya Ja Hankulan Masu Kallo A Nijeriya

August 31, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hatsarin Jirgi: Babu Batun Zagon-Æ™asa Ga Harkokin Sufurin Jiragen Ƙasan Abuja-Kaduna – Gwamnati

August 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.