• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihohin Arewa Za Su Ware Kaso 5 Na Kasafi Don Taimaka Wa ‘Yan Gudun Hijira

by Khalid Idris Doya
1 year ago
arewa

Gwamnonin jihohin Adamawa, Benuwai, Borno da Yobe sun sha alwashin ware kaso sama da biyar daga cikin kasafin kudin jihohinsu domin taimaka wa rayuwar ‘yan gudun hijira sama da miliyan hudu da suke zaman neman mafaka a jihohinsu.

Gwamnonin sun sha alwashin ne yayin wani taron kaddamar da shiri na musamman domin nemi mafita mai dorewa kan halin da ‘yan gudun hijira ke ciki da ya gudana a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

  • Taron Gwamnonin Arewa Maso Gabas Karo Na 10, Me Ya Kamata Ku Sani?
  • Mun Rage Barazanar Ƴan Bindiga Da 70% A Jihar Katsina – Gwamna Radda

Da take magana a yayin taron ta yanar gizo, mataimakiyar babban sakataren majalisar dinkin duniya, Amina Mohammed, ta ce lalubo bakin zaren shawo kan matsalolin na ‘yan gudun hijira na daga cikin muhimman abubuwan da ya kamata Nijeriya ta sanya a gaba kuma ita kanta majalisar dinkin duniya ta damu da lamarin.

Ta lura kan cewa adadin ‘yan gudun hijira ya ninku a cikin shekaru goma da ya kai kusan mutum miliyan 76 da suke halin gudun hijira a fadin duniya.

“Sama da ‘yan Nijeriya miliyan hudu na neman mafita zuwa inda aka tilasta musu yin kaura na dole,” ta ce, tsarin a matakin farko zai ba da mafita kan yadda za a nemi hanyoyin magance matsalolin da suka shafi na mutanen.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar Kare Ƴancin Masu Amfani Da Kaya (FCCPC): Tabbatar Da Adalci A Kasuwa

Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu

Tun da farko a jawabinsa, mukaddashin babban sakataren majalisar dinkin duniya kuma mashawarci kan nemo mafita mai dorewa, Mista Robert Piper, ya jinjina wa irin azamar gwamnatin Nijeriya da shugabanninta wajen ganin sun zama kasa ta farko a cikin kasashe 15 wajen kaddamar da shirin neman mafita mai dorewa ga ‘yan gudun hijira.

Piper ya ce kaddamar da shirin wata alama ce da ke nuni da cewa tabbas ‘yan siyasan da suke kan mulki a yanzu sun himmatu wajen ganin sun taimaka wa ‘yan gudun hijira da nema musu mafita a Nijeriya. Ya ce, dabarbaru da hikimomin yadda za a bi duk suna kunshe cikin shirin.

Shi kuma a nasa bangaren, mataimakin shugaban kasar Nijeriya, Sanata Kashim Shettima, ya yi kira ne na samar da hadin guiwa a duniyance wajen ganin an shawo kan matsalolin ‘yan gudun hijara a Nijeriya.
Ya ce, gwamnatin tarayya ta himmatu ainun wajen ganin ta kyautata da kare rayuwar ‘yan gudun hijira.

Da yake kaddamar da shirin da za a aiwatar a jihohi hudu da suke arewa Adamawa, Benuwai, Borno da Yobe, Shettima ya ce, babu yadda za a yi gwamnati ta dage idonta daga kan ‘yan gudun hijira ko daina damuwa da matsalolinsu, a maimakon hakan ya tabbatar da cewa dole ne a kare rayuwar kowani dan kasa.

Shi kuma a nasa bangaren, gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya ce, gwamnatin jihar a shirye take dari bisa dari wajen aiwatar da shirin da aka tsara domin nemo mafita. Ya ce, gwamnatinsa za ta iya ware kaso mai tsoka fiye da yadda ake tsammani domin nasarar shirin.

Zulum ya ce, gwamnatinsa tana kokarin yadda za su maida ‘yan gudun hijira garuruwansu na asali domin ci gaba da gudanar da harkokin rayuwarsu.

Shi ma gwamna Jihar Benuwai, Hyacinth Alia ya ce, kaddamar da shirin zai taimaka sosai wajen kyautata rayuwa da jin dadin al’umman da suke jiharsa.

Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni ya ce, sun maida hankali wajen gudanar da ayyukan da kai tsaye za su kyautata da inganta rayuwar al’ummarsu, don haka a shirye suke su mara wa shirin kyautata rayuwar ‘yan gudun hijira baya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Labarai

Hukumar Kare Ƴancin Masu Amfani Da Kaya (FCCPC): Tabbatar Da Adalci A Kasuwa

October 25, 2025
Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu
Manyan Labarai

Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025 Dakta Tony Okpanachi

October 25, 2025
Next Post
iyakokin kasa

Na’urorin Kula Da Iyakokin Kasa Za Su Fara Aiki Ba Da Jimawa Ba – Ministan Cikin Gida

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Hukumar Kare Ƴancin Masu Amfani Da Kaya (FCCPC): Tabbatar Da Adalci A Kasuwa

October 25, 2025
Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu

Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025 Dakta Tony Okpanachi

October 25, 2025
Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin

Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Shugaban Kamfani Na Shekarar 2025 Gbenga Olu Komolafe

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Thomas Etuh: Gwarzon Ɗan Kasuwa Na 2025

October 25, 2025
Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

October 25, 2025
Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.