• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihohin Nijeriya 10 Da Ke Kan Gaba A Yawan Bashi

by Bello Hamza
1 year ago
in Tattalin Arziki
0
bashi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanaki ne Ofishin Kula da Basuka na Kasa (DMO) ta bayar da kididdgar yawan basukan da ake bin jihohi 36 na kasar nan inda ya ce, basukan da ke bin jihohji 36 da babbar birnin tarayya Abuja ya kai Dala Biliyan 4.61 lamarin kuma yana ta karuwa. An dai fitar da kididigar ne a ranar 31 Disamba 2023.
Bayanin ya nuna cewa, jihohi 10 da suke kan gaba a yawan basuka a Nijeriya sun kasance kamar haka:

Jihar Anambara
Jihar Anambara ce ta 10 a jerin jihohi 10 da ke dauke da yawan basuka a Nijeriya inda take da basukan kasashen waje na Dala miliyan 107.24 a daidai karshen shekarar 2023, wannan ya nuna yadda basukan suka karu daga yadda yake na dala miliyan 103.82 a shekarar 2022.

Jihar Kano
Bashin da ake bin Jihar Kano ya kai Dala miliyan 107.92 a shekarar 2023, wanda hakan ke nuna karin kashi 7.2 na abin da ke bin jihar a shekarar 2022 (Na miliyan 100.67).

Jihar Inugu
Allah ya albarkaci Jihar Inugu da ma’adanin Kwal, bayani ya kuma nuna an dan samu raguwa a basukan da ake bin jihar a kasashen ketare, inda ake binta dala miliyan 120.86 a shekarar 2022 ya kuma ragu zuwa dala miliyan 120.45 a shekarar 2023. Wannan dan raguwar da aka samu yana nuna irin yadda gwamnatin jihar ke alkinta albarkatun jihar.

Jihar Ekiti
Basukan da ake bin Jihar Ekiti ya matukar karuwa. Basukanta na kasashen waje ya kai Dala miliyan 121.05 a shekarar 2023. Amma a shekarar 2022 kudin da ke kan jihar da sunan bashi ya kai Dala miliyan 105.59, abin da ke nuna irin karuwar da aka samu.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

Jihar Ogun
Jihar Ogun mai makwabtaka da Jihar Legas da ke tashen bunkasar tattalin arziki tana da basukan kasashen waje da ya kai na dala miliyan 168.83 a shekarar 2023, wannan na nuna karin da aka samu a kan Dala Miliyan 136.26 da ake bin jihar a shekarar 2022.

Jihar Bauchi
Bashin kasashen waje da ke bin Jihar Bauchi ya kai Dala miliyan 187.63 a shekarar 2023, an samu karin ne a kan Dala miliyan 165.78 da ake bin jihar a shekara 2022. Wannan tulin bashin na nuna bukatar da ake da shi na jihar ta kara fadada hanyoyin samar da kudaden shigarta.

Jihar Kros Ribas
Duk da albarkatun kasa da ke jawo masu zuba jari, jihar Kros Ribas ta samu karuwar basukan kasashen waje inda ake binta dala Miliyan 211.13 a shekarar 2023 daga dala miliyan 209.53 da ake binta a shekarar 2022.

Jihar Edo
Bashin kasashen waje da ke a kan Jihar Edo ya tashi zuwa dala miliyan 314.45 a shekarar 2023 daga Dala miliyan 261.15 a shekarar 2022.

Jihar Kaduna
Bashin kasashen waje da ake bin Jihar Kaduna ya kai Dala miliyan 587.07 a shekarar 2023, an samu kari a kan Dala miliyan 573.74 da ake binta a shekarar 2022.

Jihar Legas
Jihar legas ne a kan gaba a jihohin da suke dakon basukan kasashen waje inda a shekarar 2023 ake binta dala biliyan 1.24. an dan samu raguwar bashin ne inda a shekarar 2022 ake bin jihar Dala biliyan 1.25. wannan raguwar da aka samu ya faru ne saboda yadda jihar ta koma dogaro da basukan cikin gida wanda a halin yanzu ya kai Naira tiriliyan 1.05.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben Edo Da Ondo: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gana Da Hukumar Zabe

Next Post

Ba Zan Yi Gaggawar Saka Haaland Da De Bruyne A Wasanninmu Ba – Guardiola

Related

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

35 minutes ago
Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

1 week ago
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

2 weeks ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

1 month ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

1 month ago
Next Post
Ba Zan Yi Gaggawar Saka Haaland Da De Bruyne A Wasanninmu Ba – Guardiola

Ba Zan Yi Gaggawar Saka Haaland Da De Bruyne A Wasanninmu Ba - Guardiola

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
bashi

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.