• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihohin Nijeriya 10 Da Ke Kan Gaba A Yawan Bashi

by Bello Hamza
1 year ago
in Tattalin Arziki
0
bashi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanaki ne Ofishin Kula da Basuka na Kasa (DMO) ta bayar da kididdgar yawan basukan da ake bin jihohi 36 na kasar nan inda ya ce, basukan da ke bin jihohji 36 da babbar birnin tarayya Abuja ya kai Dala Biliyan 4.61 lamarin kuma yana ta karuwa. An dai fitar da kididigar ne a ranar 31 Disamba 2023.
Bayanin ya nuna cewa, jihohi 10 da suke kan gaba a yawan basuka a Nijeriya sun kasance kamar haka:

Jihar Anambara
Jihar Anambara ce ta 10 a jerin jihohi 10 da ke dauke da yawan basuka a Nijeriya inda take da basukan kasashen waje na Dala miliyan 107.24 a daidai karshen shekarar 2023, wannan ya nuna yadda basukan suka karu daga yadda yake na dala miliyan 103.82 a shekarar 2022.

Jihar Kano
Bashin da ake bin Jihar Kano ya kai Dala miliyan 107.92 a shekarar 2023, wanda hakan ke nuna karin kashi 7.2 na abin da ke bin jihar a shekarar 2022 (Na miliyan 100.67).

Jihar Inugu
Allah ya albarkaci Jihar Inugu da ma’adanin Kwal, bayani ya kuma nuna an dan samu raguwa a basukan da ake bin jihar a kasashen ketare, inda ake binta dala miliyan 120.86 a shekarar 2022 ya kuma ragu zuwa dala miliyan 120.45 a shekarar 2023. Wannan dan raguwar da aka samu yana nuna irin yadda gwamnatin jihar ke alkinta albarkatun jihar.

Jihar Ekiti
Basukan da ake bin Jihar Ekiti ya matukar karuwa. Basukanta na kasashen waje ya kai Dala miliyan 121.05 a shekarar 2023. Amma a shekarar 2022 kudin da ke kan jihar da sunan bashi ya kai Dala miliyan 105.59, abin da ke nuna irin karuwar da aka samu.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

Jihar Ogun
Jihar Ogun mai makwabtaka da Jihar Legas da ke tashen bunkasar tattalin arziki tana da basukan kasashen waje da ya kai na dala miliyan 168.83 a shekarar 2023, wannan na nuna karin da aka samu a kan Dala Miliyan 136.26 da ake bin jihar a shekarar 2022.

Jihar Bauchi
Bashin kasashen waje da ke bin Jihar Bauchi ya kai Dala miliyan 187.63 a shekarar 2023, an samu karin ne a kan Dala miliyan 165.78 da ake bin jihar a shekara 2022. Wannan tulin bashin na nuna bukatar da ake da shi na jihar ta kara fadada hanyoyin samar da kudaden shigarta.

Jihar Kros Ribas
Duk da albarkatun kasa da ke jawo masu zuba jari, jihar Kros Ribas ta samu karuwar basukan kasashen waje inda ake binta dala Miliyan 211.13 a shekarar 2023 daga dala miliyan 209.53 da ake binta a shekarar 2022.

Jihar Edo
Bashin kasashen waje da ke a kan Jihar Edo ya tashi zuwa dala miliyan 314.45 a shekarar 2023 daga Dala miliyan 261.15 a shekarar 2022.

Jihar Kaduna
Bashin kasashen waje da ake bin Jihar Kaduna ya kai Dala miliyan 587.07 a shekarar 2023, an samu kari a kan Dala miliyan 573.74 da ake binta a shekarar 2022.

Jihar Legas
Jihar legas ne a kan gaba a jihohin da suke dakon basukan kasashen waje inda a shekarar 2023 ake binta dala biliyan 1.24. an dan samu raguwar bashin ne inda a shekarar 2022 ake bin jihar Dala biliyan 1.25. wannan raguwar da aka samu ya faru ne saboda yadda jihar ta koma dogaro da basukan cikin gida wanda a halin yanzu ya kai Naira tiriliyan 1.05.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben Edo Da Ondo: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gana Da Hukumar Zabe

Next Post

Ba Zan Yi Gaggawar Saka Haaland Da De Bruyne A Wasanninmu Ba – Guardiola

Related

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

2 weeks ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

2 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

3 weeks ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA

3 weeks ago
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Bukaci ‘Yan Kasuwa Su Yi Amafani Da Damar Fitar Da Kaya Zuwa Ketare

4 weeks ago
Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97
Tattalin Arziki

Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97

4 weeks ago
Next Post
Ba Zan Yi Gaggawar Saka Haaland Da De Bruyne A Wasanninmu Ba – Guardiola

Ba Zan Yi Gaggawar Saka Haaland Da De Bruyne A Wasanninmu Ba - Guardiola

LABARAI MASU NASABA

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.