ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihohin Nijeriya 10 Da Ke Kan Gaba A Yawan Bashi

by Bello Hamza
2 years ago
bashi

Kwanaki ne Ofishin Kula da Basuka na Kasa (DMO) ta bayar da kididdgar yawan basukan da ake bin jihohi 36 na kasar nan inda ya ce, basukan da ke bin jihohji 36 da babbar birnin tarayya Abuja ya kai Dala Biliyan 4.61 lamarin kuma yana ta karuwa. An dai fitar da kididigar ne a ranar 31 Disamba 2023.
Bayanin ya nuna cewa, jihohi 10 da suke kan gaba a yawan basuka a Nijeriya sun kasance kamar haka:

Jihar Anambara
Jihar Anambara ce ta 10 a jerin jihohi 10 da ke dauke da yawan basuka a Nijeriya inda take da basukan kasashen waje na Dala miliyan 107.24 a daidai karshen shekarar 2023, wannan ya nuna yadda basukan suka karu daga yadda yake na dala miliyan 103.82 a shekarar 2022.

Jihar Kano
Bashin da ake bin Jihar Kano ya kai Dala miliyan 107.92 a shekarar 2023, wanda hakan ke nuna karin kashi 7.2 na abin da ke bin jihar a shekarar 2022 (Na miliyan 100.67).

ADVERTISEMENT

Jihar Inugu
Allah ya albarkaci Jihar Inugu da ma’adanin Kwal, bayani ya kuma nuna an dan samu raguwa a basukan da ake bin jihar a kasashen ketare, inda ake binta dala miliyan 120.86 a shekarar 2022 ya kuma ragu zuwa dala miliyan 120.45 a shekarar 2023. Wannan dan raguwar da aka samu yana nuna irin yadda gwamnatin jihar ke alkinta albarkatun jihar.

Jihar Ekiti
Basukan da ake bin Jihar Ekiti ya matukar karuwa. Basukanta na kasashen waje ya kai Dala miliyan 121.05 a shekarar 2023. Amma a shekarar 2022 kudin da ke kan jihar da sunan bashi ya kai Dala miliyan 105.59, abin da ke nuna irin karuwar da aka samu.

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

Jihar Ogun
Jihar Ogun mai makwabtaka da Jihar Legas da ke tashen bunkasar tattalin arziki tana da basukan kasashen waje da ya kai na dala miliyan 168.83 a shekarar 2023, wannan na nuna karin da aka samu a kan Dala Miliyan 136.26 da ake bin jihar a shekarar 2022.

Jihar Bauchi
Bashin kasashen waje da ke bin Jihar Bauchi ya kai Dala miliyan 187.63 a shekarar 2023, an samu karin ne a kan Dala miliyan 165.78 da ake bin jihar a shekara 2022. Wannan tulin bashin na nuna bukatar da ake da shi na jihar ta kara fadada hanyoyin samar da kudaden shigarta.

Jihar Kros Ribas
Duk da albarkatun kasa da ke jawo masu zuba jari, jihar Kros Ribas ta samu karuwar basukan kasashen waje inda ake binta dala Miliyan 211.13 a shekarar 2023 daga dala miliyan 209.53 da ake binta a shekarar 2022.

Jihar Edo
Bashin kasashen waje da ke a kan Jihar Edo ya tashi zuwa dala miliyan 314.45 a shekarar 2023 daga Dala miliyan 261.15 a shekarar 2022.

Jihar Kaduna
Bashin kasashen waje da ake bin Jihar Kaduna ya kai Dala miliyan 587.07 a shekarar 2023, an samu kari a kan Dala miliyan 573.74 da ake binta a shekarar 2022.

Jihar Legas
Jihar legas ne a kan gaba a jihohin da suke dakon basukan kasashen waje inda a shekarar 2023 ake binta dala biliyan 1.24. an dan samu raguwar bashin ne inda a shekarar 2022 ake bin jihar Dala biliyan 1.25. wannan raguwar da aka samu ya faru ne saboda yadda jihar ta koma dogaro da basukan cikin gida wanda a halin yanzu ya kai Naira tiriliyan 1.05.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Tattalin Arziki

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025
Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

November 7, 2025
Tattalin Arziki

Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho

November 7, 2025
Next Post
Ba Zan Yi Gaggawar Saka Haaland Da De Bruyne A Wasanninmu Ba – Guardiola

Ba Zan Yi Gaggawar Saka Haaland Da De Bruyne A Wasanninmu Ba - Guardiola

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

November 12, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.