ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihohin Nijeriya 10 Da Ke Kan Gaba A Yawan Bashi

by Bello Hamza
2 years ago
bashi

Kwanaki ne Ofishin Kula da Basuka na Kasa (DMO) ta bayar da kididdgar yawan basukan da ake bin jihohi 36 na kasar nan inda ya ce, basukan da ke bin jihohji 36 da babbar birnin tarayya Abuja ya kai Dala Biliyan 4.61 lamarin kuma yana ta karuwa. An dai fitar da kididigar ne a ranar 31 Disamba 2023.
Bayanin ya nuna cewa, jihohi 10 da suke kan gaba a yawan basuka a Nijeriya sun kasance kamar haka:

Jihar Anambara
Jihar Anambara ce ta 10 a jerin jihohi 10 da ke dauke da yawan basuka a Nijeriya inda take da basukan kasashen waje na Dala miliyan 107.24 a daidai karshen shekarar 2023, wannan ya nuna yadda basukan suka karu daga yadda yake na dala miliyan 103.82 a shekarar 2022.

Jihar Kano
Bashin da ake bin Jihar Kano ya kai Dala miliyan 107.92 a shekarar 2023, wanda hakan ke nuna karin kashi 7.2 na abin da ke bin jihar a shekarar 2022 (Na miliyan 100.67).

ADVERTISEMENT

Jihar Inugu
Allah ya albarkaci Jihar Inugu da ma’adanin Kwal, bayani ya kuma nuna an dan samu raguwa a basukan da ake bin jihar a kasashen ketare, inda ake binta dala miliyan 120.86 a shekarar 2022 ya kuma ragu zuwa dala miliyan 120.45 a shekarar 2023. Wannan dan raguwar da aka samu yana nuna irin yadda gwamnatin jihar ke alkinta albarkatun jihar.

Jihar Ekiti
Basukan da ake bin Jihar Ekiti ya matukar karuwa. Basukanta na kasashen waje ya kai Dala miliyan 121.05 a shekarar 2023. Amma a shekarar 2022 kudin da ke kan jihar da sunan bashi ya kai Dala miliyan 105.59, abin da ke nuna irin karuwar da aka samu.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

Jihar Ogun
Jihar Ogun mai makwabtaka da Jihar Legas da ke tashen bunkasar tattalin arziki tana da basukan kasashen waje da ya kai na dala miliyan 168.83 a shekarar 2023, wannan na nuna karin da aka samu a kan Dala Miliyan 136.26 da ake bin jihar a shekarar 2022.

Jihar Bauchi
Bashin kasashen waje da ke bin Jihar Bauchi ya kai Dala miliyan 187.63 a shekarar 2023, an samu karin ne a kan Dala miliyan 165.78 da ake bin jihar a shekara 2022. Wannan tulin bashin na nuna bukatar da ake da shi na jihar ta kara fadada hanyoyin samar da kudaden shigarta.

Jihar Kros Ribas
Duk da albarkatun kasa da ke jawo masu zuba jari, jihar Kros Ribas ta samu karuwar basukan kasashen waje inda ake binta dala Miliyan 211.13 a shekarar 2023 daga dala miliyan 209.53 da ake binta a shekarar 2022.

Jihar Edo
Bashin kasashen waje da ke a kan Jihar Edo ya tashi zuwa dala miliyan 314.45 a shekarar 2023 daga Dala miliyan 261.15 a shekarar 2022.

Jihar Kaduna
Bashin kasashen waje da ake bin Jihar Kaduna ya kai Dala miliyan 587.07 a shekarar 2023, an samu kari a kan Dala miliyan 573.74 da ake binta a shekarar 2022.

Jihar Legas
Jihar legas ne a kan gaba a jihohin da suke dakon basukan kasashen waje inda a shekarar 2023 ake binta dala biliyan 1.24. an dan samu raguwar bashin ne inda a shekarar 2022 ake bin jihar Dala biliyan 1.25. wannan raguwar da aka samu ya faru ne saboda yadda jihar ta koma dogaro da basukan cikin gida wanda a halin yanzu ya kai Naira tiriliyan 1.05.

bashi
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

MASU ALAKA

Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024
Tattalin Arziki

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026
Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN
Tattalin Arziki

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

June 8, 2026
Next Post
Ba Zan Yi Gaggawar Saka Haaland Da De Bruyne A Wasanninmu Ba – Guardiola

Ba Zan Yi Gaggawar Saka Haaland Da De Bruyne A Wasanninmu Ba - Guardiola

LABARAI MASU NASABA

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.