Sanannen masanin harkokin kudi da zuba jari na duniya Jim Rogers, ya ce ana duba yuwuwar kara zuba jari a kasar Sin yayin da ake hasashen makoma a nan gaba.
Jim Roger ya ce, yana da hannun jari a kasar Sin, kuma yana kokarin kara zuba jari a kasuwar hannayen jari ta kasar.
Masanin wanda ya shafe shekaru sama da 20 yana zuba jari a kasar Sin, ya bayyana haka ne cikin jawabin da ya gabatar a yayin taron tattaunawa na bana, na jami’ar Yale ta Amurka da kasar Sin a makon da ya gabata, inda ya jaddada muhimmancin kasar Sin a karni na 21.
A cewarsa, idan masu zuba jari za su yi bincike, to akwai dimbin damarmaki a kasar Sin, bisa la’akari da yawan al’ummarta, kuma rashin bashi mai girma da ake binta da gibin cinikayya, sun tallafa sosai ga takardar kudin kasar wato RMB. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp