• English
  • Business News
Tuesday, September 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jita-Jitar Da Wasu Kafafen Watsa Labarai Na Kasashen Yamma Suke Bazawa Ba Su Dace Da Hakikanin Yanayin Da Xinjiang Ke Ciki Ba

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Jita-Jitar Da Wasu Kafafen Watsa Labarai Na Kasashen Yamma Suke Bazawa Ba Su Dace Da Hakikanin Yanayin Da Xinjiang Ke Ciki Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin baya ne, jakadun kasashe 25 da suka hada da Dominica da Myama da Iran suka ziyarci birnin Urumqi da yankin Kashgar da birnin Aksu na jihar Xinjiang ta kasar Sin tsakanin ranakun 31 ga watan Yuli zuwa ranar 4 ga wannan wata, bisa gayyatar da ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta yi musu, inda suka yi musaya mai zurfi da mazauna biranen ’yan kabilu daban daban, tare kuma da ganin ci gaban tattalin arziki da zaman takewar al’umma dake Xinjiang ba tare da wani shamaki ba.

Galibin jakadun sun bayyana cewa, akwai zaman jituwa a tsakanin al’ummar Xinjiang, tattalin arzikin jihar yana samun ci gaba cikin sauri, al’adun jihar sun inganta yadda ya kamata. Bugu da kari, al’ummar Xinjiang na jin dadin rayuwarsu, jita-jitar da wasu kafafen watsa labarai na kasashen yamma suke bazawa ba su dace da hakikanin yanayin da Xinjiang ke ciki ba.

  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Mutunta Ikonta Na Teku

’Yan tawagar sun kuma bayyana cewa, jihar Xinjiang da suka gani da idanunsu, ta sha bamban da yadda wasu kafafen yada labarai na yammacin duniya suke bayyana jihar Xinjiang, mai al’umma dake zaman jituwa, da tattalin arziki mai wadata, jama’ar dukkan kabilu suna zaune lami lafiya, kana ana kara yin ayyuka daban-daban.

Ban da wannan kuma, ’yan tawagar sun shaidawa taron manema labaran da aka shirya bayan kammala wannan muhimmiyar ziyara cewa, musulman Xinjiang suna da ’yancin gudanar da addini bisa doka, maganar cewa wai ana kisan kare dangi da zaluncin addini karya ce kawai aka kitsa da nufin bata sunan kasar Sin mai kaunar wanzar da zaman lafiya da samun bunkasuwa a duniya. A cikin ’yan shekarun da suka gabata, gwamnatin jihar Xinjiang ta yi kokari matuka domin yaki da ta’addanci bisa doka, kuma ta samu sakamako a zahiri.

Sanin kowa ne cewa, burin kafofin watsa labaran yammacin duniya shi ne, jirkita gaskiya game da kasashen da suke adawa da ita, ko dai suke ci gabansu ko burinsu na tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da samun wadata a duniya baki daya.

Labarai Masu Nasaba

Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

Jihar Xinjiang ta Uygur mai cin gashin kanta, wani bangare ne na kasar Sin mai kunshe da kabilu daban-daban dake zaune cikin zaman lafiya da jituwa. Amma saboda adawa da jerin abubuwan dake faruwa da wadansu da ba su taba zuwa yankin ba, suke kokarin baza karairayi da yada jita-jita.

Don haka, bai kamata ba mutane ko kasashe su rika fadin abin da ba su da masani a kai, don kawai neman biyan bukatunsu na siyasa. Gani da ido aka ce maganin tambaya, har ma ya kori ji. (Ibrahim Yaya)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Sin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wolves Ta Dauki Sabon Koci Bayan Tashin Lopetegui

Next Post

Jakadun Kasashe 25 Sun Ce Ba Su Ga Abin Da Ake Kira “Aikin Tilastawa” A Xinjiang Ba

Related

Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

11 hours ago
Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

11 hours ago
AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci
Daga Birnin Sin

AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

12 hours ago
Shugaban Zimbabwe Ya Sauka Beijing Domin Halartar Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan
Daga Birnin Sin

Shugaban Zimbabwe Ya Sauka Beijing Domin Halartar Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan

13 hours ago
Xi Ya Gabatar Da Jawabin Bude Taron Majalisar Shugabannin Kasashe Membobin Kungiyar SCO
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gabatar Da Jawabin Bude Taron Majalisar Shugabannin Kasashe Membobin Kungiyar SCO

14 hours ago
Antonio Guterres: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Sanin Ya Kamata
Daga Birnin Sin

Antonio Guterres: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Sanin Ya Kamata

16 hours ago
Next Post
Jakadun Kasashe 25 Sun Ce Ba Su Ga Abin Da Ake Kira “Aikin Tilastawa” A Xinjiang Ba

Jakadun Kasashe 25 Sun Ce Ba Su Ga Abin Da Ake Kira “Aikin Tilastawa” A Xinjiang Ba

LABARAI MASU NASABA

Zargin Cin Hanci: Babu Wani Shirin Tsige El-Rufai – Kakakin Majalisar Dokokin Kaduna

Gwamnatin Kaduna Ta Gargaɗi El-Rufai Kan Yunƙurin Tayar Da Rikici A Jihar

September 2, 2025
Za Mu Taimaka PDP Ta Fadi Zaben 2023 -Wike

2027: Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Zawarcin Peter Obi

September 2, 2025
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Daba 107 A Kano, Sun Ƙwato Makamai Da Ƙwayoyi

September 2, 2025
Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

September 1, 2025
Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

September 1, 2025
Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

September 1, 2025
AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

September 1, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Da Ƙarin Kasafin Naira Biliyan 215.3 A Na 2025

September 1, 2025
Shugaban Zimbabwe Ya Sauka Beijing Domin Halartar Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan

Shugaban Zimbabwe Ya Sauka Beijing Domin Halartar Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan

September 1, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mata Da Yara A Zamfara

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mata Da Yara A Zamfara

September 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.