ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jita-Jitar Da Wasu Kafafen Watsa Labarai Na Kasashen Yamma Suke Bazawa Ba Su Dace Da Hakikanin Yanayin Da Xinjiang Ke Ciki Ba

by CMG Hausa
3 years ago
Xinjiang

A kwanakin baya ne, jakadun kasashe 25 da suka hada da Dominica da Myama da Iran suka ziyarci birnin Urumqi da yankin Kashgar da birnin Aksu na jihar Xinjiang ta kasar Sin tsakanin ranakun 31 ga watan Yuli zuwa ranar 4 ga wannan wata, bisa gayyatar da ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta yi musu, inda suka yi musaya mai zurfi da mazauna biranen ’yan kabilu daban daban, tare kuma da ganin ci gaban tattalin arziki da zaman takewar al’umma dake Xinjiang ba tare da wani shamaki ba.

Galibin jakadun sun bayyana cewa, akwai zaman jituwa a tsakanin al’ummar Xinjiang, tattalin arzikin jihar yana samun ci gaba cikin sauri, al’adun jihar sun inganta yadda ya kamata. Bugu da kari, al’ummar Xinjiang na jin dadin rayuwarsu, jita-jitar da wasu kafafen watsa labarai na kasashen yamma suke bazawa ba su dace da hakikanin yanayin da Xinjiang ke ciki ba.

  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Mutunta Ikonta Na Teku

’Yan tawagar sun kuma bayyana cewa, jihar Xinjiang da suka gani da idanunsu, ta sha bamban da yadda wasu kafafen yada labarai na yammacin duniya suke bayyana jihar Xinjiang, mai al’umma dake zaman jituwa, da tattalin arziki mai wadata, jama’ar dukkan kabilu suna zaune lami lafiya, kana ana kara yin ayyuka daban-daban.

ADVERTISEMENT

Ban da wannan kuma, ’yan tawagar sun shaidawa taron manema labaran da aka shirya bayan kammala wannan muhimmiyar ziyara cewa, musulman Xinjiang suna da ’yancin gudanar da addini bisa doka, maganar cewa wai ana kisan kare dangi da zaluncin addini karya ce kawai aka kitsa da nufin bata sunan kasar Sin mai kaunar wanzar da zaman lafiya da samun bunkasuwa a duniya. A cikin ’yan shekarun da suka gabata, gwamnatin jihar Xinjiang ta yi kokari matuka domin yaki da ta’addanci bisa doka, kuma ta samu sakamako a zahiri.

Sanin kowa ne cewa, burin kafofin watsa labaran yammacin duniya shi ne, jirkita gaskiya game da kasashen da suke adawa da ita, ko dai suke ci gabansu ko burinsu na tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da samun wadata a duniya baki daya.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Jihar Xinjiang ta Uygur mai cin gashin kanta, wani bangare ne na kasar Sin mai kunshe da kabilu daban-daban dake zaune cikin zaman lafiya da jituwa. Amma saboda adawa da jerin abubuwan dake faruwa da wadansu da ba su taba zuwa yankin ba, suke kokarin baza karairayi da yada jita-jita.

Don haka, bai kamata ba mutane ko kasashe su rika fadin abin da ba su da masani a kai, don kawai neman biyan bukatunsu na siyasa. Gani da ido aka ce maganin tambaya, har ma ya kori ji. (Ibrahim Yaya)

 

Xinjiang
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Jakadun Kasashe 25 Sun Ce Ba Su Ga Abin Da Ake Kira “Aikin Tilastawa” A Xinjiang Ba

Jakadun Kasashe 25 Sun Ce Ba Su Ga Abin Da Ake Kira “Aikin Tilastawa” A Xinjiang Ba

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.