• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Juyin-juya-halin Kyautata Muhalli: Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Samar Da Makoma Mai Kyau

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Juyin-juya-halin Kyautata Muhalli: Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Samar Da Makoma Mai Kyau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasar Sin, mai mafi yawan jama’a a duniya na samun ci gaba mai ban mamaki a fannin fasahar inganta muhalli bisa yadda take bullo da sabbin hanyoyin kare muhalli da amfani da albarkatu yadda ya kamata. Ci gaban da take samu a wannan bangare na da ban sha’awa da kuma uwa-uba kyakkyawan tasiri ga makomar duniyarmu.

Kasar ta mayar da hankali kan makamashin da ake sabuntawa wanda ake samarwa daga abubuwa na asali kamar rana, iska, da ruwa. Kasar Sin ta zama kan gaba a duniya wajen amfani da makamashin da ake iya sabuntawa, musamman hasken rana da iska. Ya zuwa shekarar 2023, kasar ta kaddamar da amfani da hasken rana mai yawa a cikin gida kuma ita ce ke da kaso 50 cikin dari na adadin karfin kayayyakin samar da wutar lantarki ta iska a duniya.

  • Amurka Ba Ta Sauya Ba Ko Kadan
  • Gwamnatin Kano Ta Kaddamar Da Sabuwar Rundunar Tsaro A Jihar

Haka nan, bangaren motocin makamashin lantarki (EVs), wani sashe ne da kasar Sin ke samun ci gaba mai ban mamaki. Motoci ne da ke amfani da wutar lantarki maimakon man fetur, inda suke rage gurbata yanayi da dogaro da albarkatun mai. Kasar Sin ta zama cibiyar wasu manyan masana’antun kera motocin ta duniya kuma tana ci gaba da kakkafa tasoshin cajin motoci a sassanta domin karfafa amfani da wadannan motoci mafi dacewa da muhalli. A shekarar 2024, ta kera motoci masu amfani da sabbin makamashi fiye da miliyan 12. Kazalika, a shekarar 2023, kamfanonin kera batirin motocin na kasar sun sami ciniki a kasuwannin duniya da kaso 60 cikin dari, yayin da kuma suka samu karin kaso 30 cikin dari na adadin baturan da suke fitarwa zuwa waje a bisa mizanin shekara. Amfani da wadannan motocin na lantarki yana taimakawa wajen rage hayaki mai cutarwa da inganta lafiyar muhallin da kowa ke rayuwa a ciki.

Har ila yau, kasar Sin tana zuba jari mai kaurin gaske a fannin tsara birane mafi dacewa da lafiyar muhalli wanda ya kunshi zayyana birane da sauran garuruwa ta hanyoyin da za su dore da kuma tabbatar da kare muhalli. Misali, akwai sabbin gine-gine da yawa a kasar Sin da aka sanya masu koren rufi, wadanda aka lullube da tsirrai da ke taimakawa wajen tsotse ruwan sama, da rage zafi, da inganta yanayin iska. Bugu da kari, biranen kasar Sin sun dukufa kyautata zirga-zirgar jama’a, da hawan keke, da tafiya da kafa don rage cunkoson ababen hawa da gurbacewar yanayi.

Wani muhimmin al’amari na juyin-juya-halin kyautata lafiyar muhalli na kasar Sin shi ne dabarun sarrafa shara. Kasar na aiwatar da tsare-tsare don rage yawan sharar da kuma sake amfani da ita. Wannan yana taimakawa kwarai wajen rage yawan sharar da ake jibgewa a wurare da karfafa tattalin arziki mai kewayowa.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Jarin da kasar Sin ke zubawa wajen inganta lafiyar muhalli mai dorewa a duniya ya nuna muhimmiyar rawar da take takawa ta wannan fuskar. A shekarar 2024, kasar ta jagoranci duniya wajen zuba jarin sauya makamashi, inda ta zuba dalar Amurka biliyan 818 a wannan bangare. Wannan jarin ya sanya kasar Sin ta zama cibiyar samar da makamashi mai tsafta a duniya domin ita ke da kusan kashi 50 cikin dari na tasoshin samar da man “hydrogen” mara gurbata muhalli a duk duniya.

Kasar Sin ta nuna wa duniya kyakkyawan misali abin koyi kamar yadda Shugaba Xi na kasar ke ci gaba da yayata muhimmancin kiyaye halittun doron kasa da kuma maye makamashi mai gurbata muhalli da mai tsafta. Shi ya sa ficewa daga yarjejeniyar shawo kan sauyin yanayi da Amurka ta yi kwanan nan, babban abin kunya ne a huldar da ta shafi kasashen duniya.

Alfanun kiyaye lafiyar muhalli bai tsaya kawai ga kiwon lafiyar halittu ba, ya kuma kunshi bude sabbin damammaki na ayyukan yi da bunkasa tattalin arziki. Hakika, yana da ban sha’awa, a ga manyan kasashe suna kara yin hobbasa wajen samar da kyakkyawar makoma mai dorewa ga dukkan bil’adama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Amurka Ba Ta Sauya Ba Ko Kadan

Next Post

Zargin Daukar Nauyin Boko Haram: Tinubu Na Ganawar Sirri Da Akpabio A Villa

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

16 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

17 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

19 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

20 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

1 day ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

1 day ago
Next Post
Zargin Daukar Nauyin Boko Haram: Tinubu Na Ganawar Sirri Da Akpabio A Villa

Zargin Daukar Nauyin Boko Haram: Tinubu Na Ganawar Sirri Da Akpabio A Villa

LABARAI MASU NASABA

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.