ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Ba Ta Sauya Ba Ko Kadan

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Amurka

Hausawa kan ce “duniya juyi-juyi ne “. To, yau za mu tattauna batun da ya shafi juyi-juyi, ko kuma sauyin, da ke faruwa a duniya.

Yanzu haka ana iya ganin sauyawar yanayi dangane da kasar Amurka: Bayan da shugaba Donald Trump ya koma fadar shugabancin kasar Amurka ta White House, kasar ta riga ta janye jiki daga hukumomin kasa da kasa da suka hada da majalisar kare hakkin dan Adam dake karkashin Majalisar Dinkin Duniya, da hukumar kiwon lafiya ta duniya WHO, da yarjeniyoyin da suka hada da yarjejeniyar tinkarar sauyin yanayi ta Paris, da ta tsara ayyukan tinkarar sauyin yanayi ta Majalisar Dinkin Duniya, ta yadda kasar ta yi watsi da nauyin dake wuyanta a cikin wadannan hukumomi da yarjeniyoyin kasa da kasa. Ban da haka, matakan da Amurka din ta dauka a cikin gida na korar da ‘yan kasashen waje, da rufe hukumar raya kasa da kasa ta Amurka ta USAID suna mummunan tasiri kan kasashen Afirka. Idan mun dauki kasar Najeriya a matsayin misali, za mu ga yadda aka tsare ‘yan Najeriya fiye da dubu 200 a kasar Amurka, wadanda za a iya maida su gida. Kana dakatar da aikin USAID ita ma ta haddasa gibin kudin da ake bukata wajen gudanar da ayyukan tinkarar cutar kanjamau, da ta tibi, da ta zazzabin cizon sauro, a kasar ta Najeriya.

  • Mutane Da Dama Sun Jikkata Sakamakon Fashewar Wani Abu A Kasuwar Zamfara
  • Gwamnatin Kebbi Ta Samar Da Tirela 300 Na Abinci Don Rabo Da Azumi

Sai dai sauyawar manufofi ba ta nufin canzawar halayyar kasar Amurka. Hakika yadda Amurka din ta yi fatali da nauyinta a cikin hukumomin kasa da kasa, da aikin kulawa da ‘yan kasashen waje, da tallafin da take samar wa sauran kasashe, ya nuna cewa, kasar sam ba ta canza manufarta ta daukar matakan kashin kai ba. Dangane da batun, jaridar Daily Trust ta kasar Najeriya ta ce abun da kasar Amurka ta yi, shi ne cire “rigarta” ta karamci. Yayin da a nata bangare, jaridar The Independent ta kasar Uganda ta ce yadda aka rufe hukumar USAID yana da kyau, saboda kasar Amurka ta dade tana amfani da hukumar wajen bayyana kanta a matsayin wata kasa “mai tausayi”, inda aka rubuta cewa, “Kasar Amurka ta ware dala kusan biliyan 900 duk shekara ga bangaren aikin soja, don jefa boma-bomai da kashe fararen hula a wurare daban daban, yayin da a nata bangaren hukumar USAID ta kashe dala biliyan 40 a kowace shekara, sa’an nan ta sanya mutane da yawa amincewa da matsayin kasar Amurka na ‘mai tausayi’.” To, daga yin kisa yadda ta ga dama, da neman samun fin karfi da yin babakere, zuwa yin fatali da nauyin dake wuyanta, da mai da moriyar kasar Amurka gaban ta sauran kasashe, anya ana iya ganin sauyawar halayyar kasar Amurka a ciki? A ‘a, sam ba za a gani ba.

ADVERTISEMENT

Saboda haka, ya kamata kasashe masu tasowa su dauki matakai don tinkarar manufofin kasar Amurka na kashin kai, wadanda ba za ta taba canzawa ba, maimakon mai da hankali kan wasu manufofin kasar na gajeren lokaci, wadanda ke sauyawa har kullum. Amma ta yaya za a iya tinkarar manufar kasar ta kashin kai? Shawara daga kasar Sin ita ce, a dauki manufar cudanyar sassa daban daban.

Ma’anar manufar ita ce, a yi kokarin samar da dabarar daidaita al’amura ta hanyar tattaunawa. Kana bangarori daban daban su samu damar tsara ka’idoji, wadanda za a bi su tare. Ban da haka, bai kamata a ba kasashe kalilan ikon tillastawa sauran kasashe wasu ka’idoji, ko kuma ba wasu kasashe masu karfi ikon ba da umarni ba. Tsakanin manufar nan da ta kashin kai, za a ga wata na dora muhimmanci kan hadin kai, yayin da wata ke daukaka fin karfi da ja-in-ja. Saboda haka cikin sauki za a iya bambance su, da ganin wanne ne daga cikinsu ya fi nuna yanayi na adalci.

LABARAI MASU NASABA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

Ban da haka, idan mun mai da hankali kan cudanyar kasashe daban daban, da zamansu tare a cikin duniya, za mu san huldar da ake da ita tare da Amurka, wani bangare ne kawai na huldar kasa da kasa. Saboda haka, yayin da wata kasa ta gamu da matsala, idan wata kasa ta nade hannu, ba ta son ba da taimako, tabbas ba za a rasa bangarorin da ke son samar da taimakon ba. Matukar an yi kokarin kulla abokantaka bisa ra’ayi na daidaiwa daida, da amfanawa kowa, to, tabbas ba za a rasa abokin hulda ba.

Sai dai idan mun nazarci sabbin matakan gwamnatin kasar Amurka, za mu ga kusan dukkansu na da nufin tsimin kudi da tabbatar da karin kudin shiga, inda ake iya ganin alamar sauyawar matsayin kasar daga mai cikakken yakini zuwa mai ra’ayin rikau, har ma ta yi watsi da kimarta da kwarjininta. Dalilin da ya sa Amurka yin haka, shi ne, ci gaban kasashe masu tasowa bisa hadin gwiwarsu na haifar da ainihin sauyawar yanayi ga tsare-tsaren kasa da kasa. (Bello Wang)

 

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

MASU ALAKA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

May 15, 2026
Next Post
Juyin-juya-halin Kyautata Muhalli: Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Samar Da Makoma Mai Kyau

Juyin-juya-halin Kyautata Muhalli: Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Samar Da Makoma Mai Kyau

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.