ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Ba Ta Sauya Ba Ko Kadan

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Amurka

Hausawa kan ce “duniya juyi-juyi ne “. To, yau za mu tattauna batun da ya shafi juyi-juyi, ko kuma sauyin, da ke faruwa a duniya.

Yanzu haka ana iya ganin sauyawar yanayi dangane da kasar Amurka: Bayan da shugaba Donald Trump ya koma fadar shugabancin kasar Amurka ta White House, kasar ta riga ta janye jiki daga hukumomin kasa da kasa da suka hada da majalisar kare hakkin dan Adam dake karkashin Majalisar Dinkin Duniya, da hukumar kiwon lafiya ta duniya WHO, da yarjeniyoyin da suka hada da yarjejeniyar tinkarar sauyin yanayi ta Paris, da ta tsara ayyukan tinkarar sauyin yanayi ta Majalisar Dinkin Duniya, ta yadda kasar ta yi watsi da nauyin dake wuyanta a cikin wadannan hukumomi da yarjeniyoyin kasa da kasa. Ban da haka, matakan da Amurka din ta dauka a cikin gida na korar da ‘yan kasashen waje, da rufe hukumar raya kasa da kasa ta Amurka ta USAID suna mummunan tasiri kan kasashen Afirka. Idan mun dauki kasar Najeriya a matsayin misali, za mu ga yadda aka tsare ‘yan Najeriya fiye da dubu 200 a kasar Amurka, wadanda za a iya maida su gida. Kana dakatar da aikin USAID ita ma ta haddasa gibin kudin da ake bukata wajen gudanar da ayyukan tinkarar cutar kanjamau, da ta tibi, da ta zazzabin cizon sauro, a kasar ta Najeriya.

  • Mutane Da Dama Sun Jikkata Sakamakon Fashewar Wani Abu A Kasuwar Zamfara
  • Gwamnatin Kebbi Ta Samar Da Tirela 300 Na Abinci Don Rabo Da Azumi

Sai dai sauyawar manufofi ba ta nufin canzawar halayyar kasar Amurka. Hakika yadda Amurka din ta yi fatali da nauyinta a cikin hukumomin kasa da kasa, da aikin kulawa da ‘yan kasashen waje, da tallafin da take samar wa sauran kasashe, ya nuna cewa, kasar sam ba ta canza manufarta ta daukar matakan kashin kai ba. Dangane da batun, jaridar Daily Trust ta kasar Najeriya ta ce abun da kasar Amurka ta yi, shi ne cire “rigarta” ta karamci. Yayin da a nata bangare, jaridar The Independent ta kasar Uganda ta ce yadda aka rufe hukumar USAID yana da kyau, saboda kasar Amurka ta dade tana amfani da hukumar wajen bayyana kanta a matsayin wata kasa “mai tausayi”, inda aka rubuta cewa, “Kasar Amurka ta ware dala kusan biliyan 900 duk shekara ga bangaren aikin soja, don jefa boma-bomai da kashe fararen hula a wurare daban daban, yayin da a nata bangaren hukumar USAID ta kashe dala biliyan 40 a kowace shekara, sa’an nan ta sanya mutane da yawa amincewa da matsayin kasar Amurka na ‘mai tausayi’.” To, daga yin kisa yadda ta ga dama, da neman samun fin karfi da yin babakere, zuwa yin fatali da nauyin dake wuyanta, da mai da moriyar kasar Amurka gaban ta sauran kasashe, anya ana iya ganin sauyawar halayyar kasar Amurka a ciki? A ‘a, sam ba za a gani ba.

ADVERTISEMENT

Saboda haka, ya kamata kasashe masu tasowa su dauki matakai don tinkarar manufofin kasar Amurka na kashin kai, wadanda ba za ta taba canzawa ba, maimakon mai da hankali kan wasu manufofin kasar na gajeren lokaci, wadanda ke sauyawa har kullum. Amma ta yaya za a iya tinkarar manufar kasar ta kashin kai? Shawara daga kasar Sin ita ce, a dauki manufar cudanyar sassa daban daban.

Ma’anar manufar ita ce, a yi kokarin samar da dabarar daidaita al’amura ta hanyar tattaunawa. Kana bangarori daban daban su samu damar tsara ka’idoji, wadanda za a bi su tare. Ban da haka, bai kamata a ba kasashe kalilan ikon tillastawa sauran kasashe wasu ka’idoji, ko kuma ba wasu kasashe masu karfi ikon ba da umarni ba. Tsakanin manufar nan da ta kashin kai, za a ga wata na dora muhimmanci kan hadin kai, yayin da wata ke daukaka fin karfi da ja-in-ja. Saboda haka cikin sauki za a iya bambance su, da ganin wanne ne daga cikinsu ya fi nuna yanayi na adalci.

LABARAI MASU NASABA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

Ban da haka, idan mun mai da hankali kan cudanyar kasashe daban daban, da zamansu tare a cikin duniya, za mu san huldar da ake da ita tare da Amurka, wani bangare ne kawai na huldar kasa da kasa. Saboda haka, yayin da wata kasa ta gamu da matsala, idan wata kasa ta nade hannu, ba ta son ba da taimako, tabbas ba za a rasa bangarorin da ke son samar da taimakon ba. Matukar an yi kokarin kulla abokantaka bisa ra’ayi na daidaiwa daida, da amfanawa kowa, to, tabbas ba za a rasa abokin hulda ba.

Sai dai idan mun nazarci sabbin matakan gwamnatin kasar Amurka, za mu ga kusan dukkansu na da nufin tsimin kudi da tabbatar da karin kudin shiga, inda ake iya ganin alamar sauyawar matsayin kasar daga mai cikakken yakini zuwa mai ra’ayin rikau, har ma ta yi watsi da kimarta da kwarjininta. Dalilin da ya sa Amurka yin haka, shi ne, ci gaban kasashe masu tasowa bisa hadin gwiwarsu na haifar da ainihin sauyawar yanayi ga tsare-tsaren kasa da kasa. (Bello Wang)

 

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026
  • Sulaiman
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • Sulaiman
    Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo
  • Sulaiman
    Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

MASU ALAKA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
Ra'ayinmu

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba
Ra'ayinmu

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

July 3, 2026
sikila
Ra'ayinmu

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026
Next Post
Juyin-juya-halin Kyautata Muhalli: Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Samar Da Makoma Mai Kyau

Juyin-juya-halin Kyautata Muhalli: Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Samar Da Makoma Mai Kyau

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.