ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Ba Ta Sauya Ba Ko Kadan

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Amurka

Hausawa kan ce “duniya juyi-juyi ne “. To, yau za mu tattauna batun da ya shafi juyi-juyi, ko kuma sauyin, da ke faruwa a duniya.

Yanzu haka ana iya ganin sauyawar yanayi dangane da kasar Amurka: Bayan da shugaba Donald Trump ya koma fadar shugabancin kasar Amurka ta White House, kasar ta riga ta janye jiki daga hukumomin kasa da kasa da suka hada da majalisar kare hakkin dan Adam dake karkashin Majalisar Dinkin Duniya, da hukumar kiwon lafiya ta duniya WHO, da yarjeniyoyin da suka hada da yarjejeniyar tinkarar sauyin yanayi ta Paris, da ta tsara ayyukan tinkarar sauyin yanayi ta Majalisar Dinkin Duniya, ta yadda kasar ta yi watsi da nauyin dake wuyanta a cikin wadannan hukumomi da yarjeniyoyin kasa da kasa. Ban da haka, matakan da Amurka din ta dauka a cikin gida na korar da ‘yan kasashen waje, da rufe hukumar raya kasa da kasa ta Amurka ta USAID suna mummunan tasiri kan kasashen Afirka. Idan mun dauki kasar Najeriya a matsayin misali, za mu ga yadda aka tsare ‘yan Najeriya fiye da dubu 200 a kasar Amurka, wadanda za a iya maida su gida. Kana dakatar da aikin USAID ita ma ta haddasa gibin kudin da ake bukata wajen gudanar da ayyukan tinkarar cutar kanjamau, da ta tibi, da ta zazzabin cizon sauro, a kasar ta Najeriya.

  • Mutane Da Dama Sun Jikkata Sakamakon Fashewar Wani Abu A Kasuwar Zamfara
  • Gwamnatin Kebbi Ta Samar Da Tirela 300 Na Abinci Don Rabo Da Azumi

Sai dai sauyawar manufofi ba ta nufin canzawar halayyar kasar Amurka. Hakika yadda Amurka din ta yi fatali da nauyinta a cikin hukumomin kasa da kasa, da aikin kulawa da ‘yan kasashen waje, da tallafin da take samar wa sauran kasashe, ya nuna cewa, kasar sam ba ta canza manufarta ta daukar matakan kashin kai ba. Dangane da batun, jaridar Daily Trust ta kasar Najeriya ta ce abun da kasar Amurka ta yi, shi ne cire “rigarta” ta karamci. Yayin da a nata bangare, jaridar The Independent ta kasar Uganda ta ce yadda aka rufe hukumar USAID yana da kyau, saboda kasar Amurka ta dade tana amfani da hukumar wajen bayyana kanta a matsayin wata kasa “mai tausayi”, inda aka rubuta cewa, “Kasar Amurka ta ware dala kusan biliyan 900 duk shekara ga bangaren aikin soja, don jefa boma-bomai da kashe fararen hula a wurare daban daban, yayin da a nata bangaren hukumar USAID ta kashe dala biliyan 40 a kowace shekara, sa’an nan ta sanya mutane da yawa amincewa da matsayin kasar Amurka na ‘mai tausayi’.” To, daga yin kisa yadda ta ga dama, da neman samun fin karfi da yin babakere, zuwa yin fatali da nauyin dake wuyanta, da mai da moriyar kasar Amurka gaban ta sauran kasashe, anya ana iya ganin sauyawar halayyar kasar Amurka a ciki? A ‘a, sam ba za a gani ba.

ADVERTISEMENT

Saboda haka, ya kamata kasashe masu tasowa su dauki matakai don tinkarar manufofin kasar Amurka na kashin kai, wadanda ba za ta taba canzawa ba, maimakon mai da hankali kan wasu manufofin kasar na gajeren lokaci, wadanda ke sauyawa har kullum. Amma ta yaya za a iya tinkarar manufar kasar ta kashin kai? Shawara daga kasar Sin ita ce, a dauki manufar cudanyar sassa daban daban.

Ma’anar manufar ita ce, a yi kokarin samar da dabarar daidaita al’amura ta hanyar tattaunawa. Kana bangarori daban daban su samu damar tsara ka’idoji, wadanda za a bi su tare. Ban da haka, bai kamata a ba kasashe kalilan ikon tillastawa sauran kasashe wasu ka’idoji, ko kuma ba wasu kasashe masu karfi ikon ba da umarni ba. Tsakanin manufar nan da ta kashin kai, za a ga wata na dora muhimmanci kan hadin kai, yayin da wata ke daukaka fin karfi da ja-in-ja. Saboda haka cikin sauki za a iya bambance su, da ganin wanne ne daga cikinsu ya fi nuna yanayi na adalci.

LABARAI MASU NASABA

Batun Shayar Da Jarirai Nonon Uwa Da Ƙalubalen Abinci Mai Gina Jiki

Buƙatar Kawo Ƙarshen Dogon Layi A Tashoshin Sayen Iskar CNG

Ban da haka, idan mun mai da hankali kan cudanyar kasashe daban daban, da zamansu tare a cikin duniya, za mu san huldar da ake da ita tare da Amurka, wani bangare ne kawai na huldar kasa da kasa. Saboda haka, yayin da wata kasa ta gamu da matsala, idan wata kasa ta nade hannu, ba ta son ba da taimako, tabbas ba za a rasa bangarorin da ke son samar da taimakon ba. Matukar an yi kokarin kulla abokantaka bisa ra’ayi na daidaiwa daida, da amfanawa kowa, to, tabbas ba za a rasa abokin hulda ba.

Sai dai idan mun nazarci sabbin matakan gwamnatin kasar Amurka, za mu ga kusan dukkansu na da nufin tsimin kudi da tabbatar da karin kudin shiga, inda ake iya ganin alamar sauyawar matsayin kasar daga mai cikakken yakini zuwa mai ra’ayin rikau, har ma ta yi watsi da kimarta da kwarjininta. Dalilin da ya sa Amurka yin haka, shi ne, ci gaban kasashe masu tasowa bisa hadin gwiwarsu na haifar da ainihin sauyawar yanayi ga tsare-tsaren kasa da kasa. (Bello Wang)

 

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Amurka
Ra'ayinmu

Batun Shayar Da Jarirai Nonon Uwa Da Ƙalubalen Abinci Mai Gina Jiki

August 14, 2026
Buƙatar Kawo Ƙarshen Dogon Layi A Tashoshin Sayen Iskar CNG
Ra'ayinmu

Buƙatar Kawo Ƙarshen Dogon Layi A Tashoshin Sayen Iskar CNG

July 31, 2026
Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
Ra'ayinmu

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Next Post
Juyin-juya-halin Kyautata Muhalli: Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Samar Da Makoma Mai Kyau

Juyin-juya-halin Kyautata Muhalli: Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Samar Da Makoma Mai Kyau

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.