• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Juyin Mulkin Nijar Da Shirin Kai Farmakin ECOWAS Sun Saba Wa Dimokuradiyya

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Juyin Mulkin Nijar Da Shirin Kai Farmakin ECOWAS Sun Saba Wa Dimokuradiyya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A matsayin ECOWAS na hukuma, an kafa ta ne domin bunkasa tattalin arziki tare da samar da hadin kai da kuma kyautata rayuwar al’ummar da ke tsakanin su. Amma manya-manyan dalililan kafa wannan gungiya sun hada da kamar haka: 

Na farko, samar da daidaito da kuma taimakekeniya a tsakanin kasashen. Na biyu, tabbatar da hadin kai tare da samar dokoki na bai-daya a tsakanin su. Na uku, kyautatawa tare da dogaro a tsakaninsu. Na hudu, tausayawa da kuma lallaba juna. Kana na biyar, tabbatar da zaman lafiya, tsaro da kwanciyar hankali.

  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Tsohowar Shugaban Kotun Gargajiya A Benue

Kungiyar Bunkasa Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), wadda aka kafa a 28 ga watan Mayun 1975, na da mambobi na kasashe goma sha biyar, a lokacin da aka kafa ta a Jihar Legas.

A matsayin ECOWAS a kungiya mai rajin samar da zaman lafiya da kwantar da tarzoma, ta tura dakarun Sojoji Kasashen Afirka daban-daban domin samar da zaman lafiya tare da kwantar da tarzoma a da, yanzu kuma za ta dirar wa Kasar Nijar da yaki.

Aikin da aka san ECOWAS da shi na tabbatar da samar da zaman lafiya da kwantar da tarzoma a tsakanin mambobinta, yanzu ya canza salo ya koma farautar su, duk dai da cewa da su da ke kokarin shiga tsakanin (ECOWAS) da kuma Sojojin da suka yi juyin mulkin, ba a doron demokradiyya suke ba. Sojojin sun saba wa demokradiyya, haka nan su ma masu kallon kawunansu a matsayin hukuma ko masu son kare muradan kawunansu.

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har ila yau ECOWAS din ta karkasu, a cikin kasashe goma sha biyar takwas ne ke kalubalantar Sojojin da suka yi juyin mulkin Nijar, amma sauran ko dai ‘yan babu ruwanmu ko kuma wadanda ke koyan bayan Nijar din kasashe kamar su Mali, Burkina Faso, Guinea da kuma Chadi, babu wani abu da suka aiwatar na rashin goyon baya ko rashin amincewa a kan wadannan Sojoji na Nijar, illa neman ba’asi na shiga tsakanin tun da farko.

Dalilin shiga tsakanin ko dagewa da Shugabannin ECOWAS din suka yi kan Nijar, domin nema wa kawunansu kariya ne sakamakon gazawarsu da kuma kashin da ke gindinsu. Wannan ce ta sa hantarsu ta kada suka shiga firgici, suke neman kariya tare da yunkurin shiga yaki na babu gaira babu dalili.

Haka zalika idan har aka sake aka shiga wannan yaki, Nijeriya ma ba za ta taba kubuta ko tsira ba, sakamon kusancin da ke tsakanin da Nijar da kuma boyayyen sirrin da ke tsakan su, kamar misali katse wutar lantarki wanda ita Nijar za ta iya samar da nata dam din wanda ka iya haifar wa da namu matsala. Don haka, alakar da ke tsakanin Nijeriya da Nijar na da karfin gaske, amma a haka ake tunanin a sa kafa a shure kawai don biyan bukatar kai da neman kariya, indai har Kasashe irin su Burkina Faso, Mali, Guinea da Chadi ba a sanya musu takunkumi ba, ya kamata ita ma Nijar a yi mata adalci a ba ta hakkinta na cikakkiyar kasa mai iko tare da ‘yanci kamar yadda sauran suke da shi.

Bai kamata mu manta cewa, Mohammad Bazoum tubabben Shugaban Kasar ta Nijar wanda ECOWAS ke son a maida wa mulki a hannunsa na hannun Sojojin da suka yi juyin mulkin ba, sannan akwai yarjejeniya a tsakanin su, saboda haka, abu mai sauki su yi garkuwa da shi. Abu mafi sauki a nan shi ne, ECOWAS ta janye dukkanin wata barazana ta tattara hankalinta wajen ganin yadda za a samu maslaha cikin ruwan sanyi don kawo karshen wannan al’amari. Idan kuwa ta gaza yin hakan, zai yi matukar wahala kungiyar ta samu hadin kan mambobinta a matsayin tan a hukuma. Babban burin ECOWAS shi ne ganin an samu zaman lafiya tare da kawar da Sojoji a Nijar su kuma tabbatar da babu abin da ya samu Shugaba Bazoum da sauran iyalansa tare da ci gaba da rayuwarsu cikin jin dadi da annashawa ba tare da an hallaka su ko wani abu makamancin haka ba.

Abraham James, Kwararre ne a kan sadarwa da harkokin Difilomasiyya da ke Nijeriya

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping: Wajibi Ne A Raya Jihar Xinjiang Yayin Da Ake Kokarin Zamanintar Da Kasa

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Gudanar Da Sallar Alkunut Domin Samun Nasarar Shari’ar Da Ake Yi A Kotu

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

14 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

14 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

16 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

16 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

18 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

19 hours ago
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Gudanar Da Sallar Alkunut Domin Samun Nasarar Shari’ar Da Ake Yi A Kotu

Gwamnatin Kano Ta Gudanar Da Sallar Alkunut Domin Samun Nasarar Shari'ar Da Ake Yi A Kotu

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.