• English
  • Business News
Tuesday, September 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

KAEDCO Za Ta Dawo Da Wutar Lantarki Cikin Sa’o’i Kadan A Jihar Kebbi – SSG 

by Sulaiman and Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
KAEDCO Za Ta Dawo Da Wutar Lantarki Cikin Sa’o’i Kadan A Jihar Kebbi – SSG 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamfanin rarraba Wutar Lantarki ta Kaduna, KAEDCO, ya amince ya maido da wutar lantarki a cikin Birnin Kebbi cikin wasu sa’o’i kadan nan gaba.

Hakan ya biyo bayan sa baki da Gwamnan Jihar Kebbi Sanata Abubakar Atiku Bagudu ya yi na sasanta rikicin da ke tsakanin kamfanin da Sojojin Nijeriya.

  • Bagudu Ya Shiga Tsakani Kan Rikicin KAEDCO Da Sojoji

Sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Babale Umar Yauri ne ya sanar da hakan bayan wata ganawa da mahukuntan KAEDCO da shugabannin rundunar sojin da sauran shugabannin hukumomin tsaro a ofishinsa da ke Birnin Kebbi.

Gwamnan ya umarci SSG da a samar da zaman lafiya tsakanin bangarorin biyu da ke rikici da juna wanda zai share fagen maido da wutar lantarki ga mazauna babban birnin jihar.

Da yake zantawa da manema labarai bayan kammala taron, Babale Umar Yauri a madadin gwamnatin jihar Kebbi ya nemi afuwar hukumar ta KAEDCO a kan abin da ya samu ma’aikatansu, tare da yin Allah wadai da irin halin da suke ciki, yana mai ba da tabbacin gwamnati da jami’an tsaro za su samar da ingantaccen tsaro ga ma’aikatan kamfanin don gudanar da ayyukansu a cikin jihar.

Labarai Masu Nasaba

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙara Kan Zargin Ƴansanda Da Cin Zarafinsa A Kaduna

Hakazalika SSG ya jaddada cewa kwamandan rundunar a Birnin Kebbi bai baiwa wani soja izinin rike ma’aikatan KAEDCO ba ballantana ya goyi bayan abin da ya faru, domin sojoji ba sa amince wa da ayyukan rashin bin doka da oda ba.

Sakataren gwamnati ya yi kira ga al’ummar jihar da su ci gaba da bin doka da oda, inda ya ce duk ma’aikacin KAEDCO da aka samu yana gudanar da ayyukansa ba bisa ka’ida ba a kai rahoto ga mahukuntan kamfanin domin daukar matakin ladabtarwa.

Ya bayyana karara cewa Gwamna Abubakar Atiku Bagudu zai ci gaba da ba da tallafin kayan aiki ga KAEDCO don tabbatar da samar da wutar lantarki akai-akai a duk sassan jihar Kebbi.

Haka Kuma ya godewa jami’an KAEDCO bisa yadda suka magance rikicin tare da nuna jin dadinsu ga jami’an soji da suka shawo kan lamarin cikin gaggawa.

A nasa jawabin, shugaban yankin KAEDCO mai kula da jihohin Sokoto, Kebbi da Zamfara, Mista Sunday Yahaya, ya yaba da fatan alheri da hakuri da gwamnatin jihar Kebbi ta yi kan wannan mummunan lamari.

Mista Sunday Yahaya ya kuma ba da hakuri cewa lamarin ya koma ga wannan matakin, amma ya yi kira ga jama’a da su ba ma’aikatan kamfanin hadin kai wajen gudanar da ayyukansu.

Shugaban yankin na KAEDCO yayin da ya umarci dukkan ma’aikatansu da su koma bakin aiki cikin gaggawa, ya shawarci masu amfani da wutar lantarki da su kai rahoton ma’aikatan KAEDCO da suka yi kura-kurai ga hukumomin da suka dace, inda ya tabbatar da cewa kamfanin yana da tsarin ladabtar da ma’aikatansa.

Taron wanda SSG ya jagoranta ya samu halartar mukaddashin shugaban ma’aikata na jihar Alhaji Safiyanu Garba Bena da wakilin kwamishinan ‘yan sanda, kwamandan rundunar sojojin na Birnin Kebbi, Kwamandan Bataliya Light Tank Battalion 223, Zuru, Wakilin Kwanturolan Kwastam, da Ma’aikatan Gudanarwa na KAEDCO.

A karshen taron bangarorin uku da aka yi tsakanin gwamnatin jihar da shugaban hukumar KAEDCO da wasu zababbun hukumomin tsaro, an rattaba hannu kan wani kudiri da dukkanin bangarorin da abin ya shafa suka sanya hannu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnati Ta Janye Tuhumar Rashawa Ta Naira Biliyan 1.84 Kan Mataimakin Dasuki Da EFCC Ke Yi Masa

Next Post

Kwararun Kasa Da Kasa: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Zaburar Da Mutane Da Yawa A Duniya

Related

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye
Manyan Labarai

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

43 minutes ago
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i
Labarai

El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙara Kan Zargin Ƴansanda Da Cin Zarafinsa A Kaduna

3 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Dage Komawa Makaranta Saboda Kidayar Jama’a
Manyan Labarai

Gini Ya Rushe A Jigawa, Mutum 1 Ya Rasu, 7 Sun Jikkata

4 hours ago
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

13 hours ago
'yansanda
Labarai

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

14 hours ago
Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai
Labarai

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

15 hours ago
Next Post
Kwararun Kasa Da Kasa: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Zaburar Da Mutane Da Yawa A Duniya

Kwararun Kasa Da Kasa: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Zaburar Da Mutane Da Yawa A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

September 9, 2025
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙara Kan Zargin Ƴansanda Da Cin Zarafinsa A Kaduna

September 9, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Dage Komawa Makaranta Saboda Kidayar Jama’a

Gini Ya Rushe A Jigawa, Mutum 1 Ya Rasu, 7 Sun Jikkata

September 9, 2025
Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

September 8, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

September 8, 2025
Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 8, 2025
'yansanda

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

September 8, 2025
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

September 8, 2025
Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

September 8, 2025
Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

September 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.