• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

KAEDCO Za Ta Dawo Da Wutar Lantarki Cikin Sa’o’i Kadan A Jihar Kebbi – SSG 

by Sulaiman and Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
KAEDCO Za Ta Dawo Da Wutar Lantarki Cikin Sa’o’i Kadan A Jihar Kebbi – SSG 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamfanin rarraba Wutar Lantarki ta Kaduna, KAEDCO, ya amince ya maido da wutar lantarki a cikin Birnin Kebbi cikin wasu sa’o’i kadan nan gaba.

Hakan ya biyo bayan sa baki da Gwamnan Jihar Kebbi Sanata Abubakar Atiku Bagudu ya yi na sasanta rikicin da ke tsakanin kamfanin da Sojojin Nijeriya.

  • Bagudu Ya Shiga Tsakani Kan Rikicin KAEDCO Da Sojoji

Sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Babale Umar Yauri ne ya sanar da hakan bayan wata ganawa da mahukuntan KAEDCO da shugabannin rundunar sojin da sauran shugabannin hukumomin tsaro a ofishinsa da ke Birnin Kebbi.

Gwamnan ya umarci SSG da a samar da zaman lafiya tsakanin bangarorin biyu da ke rikici da juna wanda zai share fagen maido da wutar lantarki ga mazauna babban birnin jihar.

Da yake zantawa da manema labarai bayan kammala taron, Babale Umar Yauri a madadin gwamnatin jihar Kebbi ya nemi afuwar hukumar ta KAEDCO a kan abin da ya samu ma’aikatansu, tare da yin Allah wadai da irin halin da suke ciki, yana mai ba da tabbacin gwamnati da jami’an tsaro za su samar da ingantaccen tsaro ga ma’aikatan kamfanin don gudanar da ayyukansu a cikin jihar.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Hakazalika SSG ya jaddada cewa kwamandan rundunar a Birnin Kebbi bai baiwa wani soja izinin rike ma’aikatan KAEDCO ba ballantana ya goyi bayan abin da ya faru, domin sojoji ba sa amince wa da ayyukan rashin bin doka da oda ba.

Sakataren gwamnati ya yi kira ga al’ummar jihar da su ci gaba da bin doka da oda, inda ya ce duk ma’aikacin KAEDCO da aka samu yana gudanar da ayyukansa ba bisa ka’ida ba a kai rahoto ga mahukuntan kamfanin domin daukar matakin ladabtarwa.

Ya bayyana karara cewa Gwamna Abubakar Atiku Bagudu zai ci gaba da ba da tallafin kayan aiki ga KAEDCO don tabbatar da samar da wutar lantarki akai-akai a duk sassan jihar Kebbi.

Haka Kuma ya godewa jami’an KAEDCO bisa yadda suka magance rikicin tare da nuna jin dadinsu ga jami’an soji da suka shawo kan lamarin cikin gaggawa.

A nasa jawabin, shugaban yankin KAEDCO mai kula da jihohin Sokoto, Kebbi da Zamfara, Mista Sunday Yahaya, ya yaba da fatan alheri da hakuri da gwamnatin jihar Kebbi ta yi kan wannan mummunan lamari.

Mista Sunday Yahaya ya kuma ba da hakuri cewa lamarin ya koma ga wannan matakin, amma ya yi kira ga jama’a da su ba ma’aikatan kamfanin hadin kai wajen gudanar da ayyukansu.

Shugaban yankin na KAEDCO yayin da ya umarci dukkan ma’aikatansu da su koma bakin aiki cikin gaggawa, ya shawarci masu amfani da wutar lantarki da su kai rahoton ma’aikatan KAEDCO da suka yi kura-kurai ga hukumomin da suka dace, inda ya tabbatar da cewa kamfanin yana da tsarin ladabtar da ma’aikatansa.

Taron wanda SSG ya jagoranta ya samu halartar mukaddashin shugaban ma’aikata na jihar Alhaji Safiyanu Garba Bena da wakilin kwamishinan ‘yan sanda, kwamandan rundunar sojojin na Birnin Kebbi, Kwamandan Bataliya Light Tank Battalion 223, Zuru, Wakilin Kwanturolan Kwastam, da Ma’aikatan Gudanarwa na KAEDCO.

A karshen taron bangarorin uku da aka yi tsakanin gwamnatin jihar da shugaban hukumar KAEDCO da wasu zababbun hukumomin tsaro, an rattaba hannu kan wani kudiri da dukkanin bangarorin da abin ya shafa suka sanya hannu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnati Ta Janye Tuhumar Rashawa Ta Naira Biliyan 1.84 Kan Mataimakin Dasuki Da EFCC Ke Yi Masa

Next Post

Kwararun Kasa Da Kasa: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Zaburar Da Mutane Da Yawa A Duniya

Related

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

2 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

4 hours ago
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

18 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

18 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

19 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

20 hours ago
Next Post
Kwararun Kasa Da Kasa: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Zaburar Da Mutane Da Yawa A Duniya

Kwararun Kasa Da Kasa: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Zaburar Da Mutane Da Yawa A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.