• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kafa Jam’iyyar Adawa: Atiku Da Wasu Sanatoci Sun Sake Sabon Yunkuri

byYusuf Shuaibu
2 years ago
Atiku

‘Yan adawa na shirin kafa sabuwar jam’iyyar domin kwace mulki daga hannun jam’iyyar APC a 2027.

Gabanin 2027, majiyoyi sun bayyana cewa dan takarar shugaban kasa na PDP a zaben da ya gabata, Alhaji Atiku Abubakar, ya hada kai da wasu ‘yan majalisa domin kafa sabuwar jam’iyya.

  • Uwargidan Shugaban Kasa Ta Bude Makaranta Ga Matan Da Aka Kora A  Manyan Makarantu A Bauchi
  • Kayayyakin Wasanni Kirar Kasar Sin Sun Samu Yabo A Gasar Wasannin Afirka Ta 13

Sun kara da cewa Atiku ya kaddamar da tawaga mai karfi domin jagorantar kafa sabuwar jam’iyyar adawa da za ta fara aiki kafin zaben 2027, inda yake tunanin cewa jam’iyyar za ta iya kwace mulki daga wurin APC.

Majiyoyin sun ce tsohon mataimakin shugaban kasan ya hada kai da tsohon gwamnan Zamfara, Abdulaziz Yari, wanda ya nemi shugabancin majalisan dattawa bai samu ba.

Haka kuma shugaban kungiyar sanatocin arewa (NSF), Abdul Ningi, zai shiga cikin wannan tawaga domin ya kasance sojon gona a zauren majalisa wajen tabbatar da sabuwar jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

A cewar masu sharhi kan al’amurar siyasa, wannan lamari na iya mammaita abun da ya faru a 2013, inda wasu gwamnoni da ‘yan majalisa suka yi wa PDP tawaye tare da yin aiki tare wajen kafa jam’iyyar APC wanda ta kwace mulki.

An dai kafa APC ne a watan Fabrairun 2013, sakamakon kwawancen jam’iyyu da suka hada da CAN, CPC, ANPP, APGA da kuma wani bangare na sabuwar PDP.

Atiku yana daga cikin wadanda suka jagoranci kafa jam’iyyar APC, inda ya tsaya takarar shugaban kasa a 2014, sai dai Muhammadu Buhari ya kayar da shi tun a zaben fitar da gwani.

Ya dai sake dawowa PDP, inda ya tsaya takara a 2019, sai dai kuma ya sha kaye a hannun Buhari. Sannan a zaben bara kuma, Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya kayar da shi.

Majiyoyin sun ce Atiku da sauran abokanansa suna kokarin maimaita abun da ya faru a 2013 na kafa sabuwar jam’iyyar kuma har da kwace mulki.

Ya ce, “Mun yi nisa kan wannan yarjejeniya. Mun tabbatar da cewa kasar nan tana cikin mummunan hali fiye da na 2014 lokacin mulkin Goodluck Ebele Jonathan, shi ya sa muka yi wannan shiri na kafa sabuwar jam’iyyar domin kwace mulki daga wurin Tinubu.”

Wani sanata daga kudu ya ce mafi yawancin abokansa suna sane da yin shiri domin mulki ya dawo arewa idan har suka samu nasarar raunata gwamnatin Tinubu a 2027.

Ya ce, “Mun san irin shirin da ake yi. Muna kallon su ne kwai. Suna ta yin siyasa wajen kawo rudani a jam’iyyarmu wanda za a ruruta wutar fada a tsakaninmu da bangaren shugaban kasa wajen tafiyar da harkokin gwamnati.

Ningi, wanda yake wakiltar Bauchi ta tsakiya a majalisar dattawa ya shaida wa sashin Hausa na BBC cewa sanatocin arewa za su yaki shugaban kasa.

Ya ce, “Lallai ba za su yaki gwamnati ba kamar yadda ‘yan adawa ke yi ba. Amma dai wannan irin sakamako ne ya dace da gwamnatin da muke da ita. Wadannan shugabannin da suke gallaza mana ba su muka zaba ba.

“Mun kawo bambance-bambancen addini da kabilanci wajen gudanar da sha’anin gwamnati. Sun kawo farfagandar cewa ba za a amince a kara bai wa Bahaushe ko Fulani shugabanci ba, saboda ba a samun zaman lafiya.

“Idan aka duba da idon basira za a ga cewa mafi yawan ‘yan adawa sun fito ne daga yankin arewa maso gabas da kuma arewa maso yamma. Amma an ki amincewa mu zama shugabannin ‘yan adawa a zauren majalisar dattawa ba.

“Wannan shi ne daya daga cikin dalilan da muka ce za mu duba mu gani kan abubuwan da ke faruwa a karkashin kungiyar sanatocin arewa, wanda nake shugabanci a yanzu haka,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Kabilu Biyar Mafiya Tsadar Aure A Nijeriya

Kabilu Biyar Mafiya Tsadar Aure A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version