• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kafa Jam’iyyar Adawa: Atiku Da Wasu Sanatoci Sun Sake Sabon Yunkuri

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Ya Kamata CBN Ya Sanya Hoton Obasanjo A Jikin Sabbin Kudin Da Za A Sauya Wa Fasali
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan adawa na shirin kafa sabuwar jam’iyyar domin kwace mulki daga hannun jam’iyyar APC a 2027.

Gabanin 2027, majiyoyi sun bayyana cewa dan takarar shugaban kasa na PDP a zaben da ya gabata, Alhaji Atiku Abubakar, ya hada kai da wasu ‘yan majalisa domin kafa sabuwar jam’iyya.

  • Uwargidan Shugaban Kasa Ta Bude Makaranta Ga Matan Da Aka Kora A  Manyan Makarantu A Bauchi
  • Kayayyakin Wasanni Kirar Kasar Sin Sun Samu Yabo A Gasar Wasannin Afirka Ta 13

Sun kara da cewa Atiku ya kaddamar da tawaga mai karfi domin jagorantar kafa sabuwar jam’iyyar adawa da za ta fara aiki kafin zaben 2027, inda yake tunanin cewa jam’iyyar za ta iya kwace mulki daga wurin APC.

Majiyoyin sun ce tsohon mataimakin shugaban kasan ya hada kai da tsohon gwamnan Zamfara, Abdulaziz Yari, wanda ya nemi shugabancin majalisan dattawa bai samu ba.

Haka kuma shugaban kungiyar sanatocin arewa (NSF), Abdul Ningi, zai shiga cikin wannan tawaga domin ya kasance sojon gona a zauren majalisa wajen tabbatar da sabuwar jam’iyyar.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

A cewar masu sharhi kan al’amurar siyasa, wannan lamari na iya mammaita abun da ya faru a 2013, inda wasu gwamnoni da ‘yan majalisa suka yi wa PDP tawaye tare da yin aiki tare wajen kafa jam’iyyar APC wanda ta kwace mulki.

An dai kafa APC ne a watan Fabrairun 2013, sakamakon kwawancen jam’iyyu da suka hada da CAN, CPC, ANPP, APGA da kuma wani bangare na sabuwar PDP.

Atiku yana daga cikin wadanda suka jagoranci kafa jam’iyyar APC, inda ya tsaya takarar shugaban kasa a 2014, sai dai Muhammadu Buhari ya kayar da shi tun a zaben fitar da gwani.

Ya dai sake dawowa PDP, inda ya tsaya takara a 2019, sai dai kuma ya sha kaye a hannun Buhari. Sannan a zaben bara kuma, Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya kayar da shi.

Majiyoyin sun ce Atiku da sauran abokanansa suna kokarin maimaita abun da ya faru a 2013 na kafa sabuwar jam’iyyar kuma har da kwace mulki.

Ya ce, “Mun yi nisa kan wannan yarjejeniya. Mun tabbatar da cewa kasar nan tana cikin mummunan hali fiye da na 2014 lokacin mulkin Goodluck Ebele Jonathan, shi ya sa muka yi wannan shiri na kafa sabuwar jam’iyyar domin kwace mulki daga wurin Tinubu.”

Wani sanata daga kudu ya ce mafi yawancin abokansa suna sane da yin shiri domin mulki ya dawo arewa idan har suka samu nasarar raunata gwamnatin Tinubu a 2027.

Ya ce, “Mun san irin shirin da ake yi. Muna kallon su ne kwai. Suna ta yin siyasa wajen kawo rudani a jam’iyyarmu wanda za a ruruta wutar fada a tsakaninmu da bangaren shugaban kasa wajen tafiyar da harkokin gwamnati.

Ningi, wanda yake wakiltar Bauchi ta tsakiya a majalisar dattawa ya shaida wa sashin Hausa na BBC cewa sanatocin arewa za su yaki shugaban kasa.

Ya ce, “Lallai ba za su yaki gwamnati ba kamar yadda ‘yan adawa ke yi ba. Amma dai wannan irin sakamako ne ya dace da gwamnatin da muke da ita. Wadannan shugabannin da suke gallaza mana ba su muka zaba ba.

“Mun kawo bambance-bambancen addini da kabilanci wajen gudanar da sha’anin gwamnati. Sun kawo farfagandar cewa ba za a amince a kara bai wa Bahaushe ko Fulani shugabanci ba, saboda ba a samun zaman lafiya.

“Idan aka duba da idon basira za a ga cewa mafi yawan ‘yan adawa sun fito ne daga yankin arewa maso gabas da kuma arewa maso yamma. Amma an ki amincewa mu zama shugabannin ‘yan adawa a zauren majalisar dattawa ba.

“Wannan shi ne daya daga cikin dalilan da muka ce za mu duba mu gani kan abubuwan da ke faruwa a karkashin kungiyar sanatocin arewa, wanda nake shugabanci a yanzu haka,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Atiku
ShareTweetSendShare
Previous Post

LEADERSHIP Ta Jinjina Wa Shehu Isma’ila Mai Diwani Kan Shafin Dausayin Musulunci

Next Post

Kabilu Biyar Mafiya Tsadar Aure A Nijeriya

Related

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

14 hours ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 week ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
Next Post
Kabilu Biyar Mafiya Tsadar Aure A Nijeriya

Kabilu Biyar Mafiya Tsadar Aure A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.