• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kalaman John Kerry Sun Nuna Girman Kai Na Kasashen Yamma

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kalaman John Kerry Sun Nuna Girman Kai Na Kasashen Yamma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kalaman da manzon musamman na shugaban kasar Amurka mai kula da aikin tinkarar sauyawar yanayi John Kerry ya furta, a taron ministocin kasashen Afirka kan aikin kare muhalli, wanda ya gudana a kasar Senegal a kwanan baya, sun ba ni mamaki sosai.

Saboda a gaban wakilan dukkan kasashen Afirka, mista Kerry ya ce kasashe masu sukuni, ba su da wani nauyi na tarihi game da batun sauyawar yanayin duniya.

  • Buhari Zai Yi Balaguro Zuwa Kasar Amurka Gobe Lahadi

A ganinsa, aikace-aikace na daukacin dan Adam ne ke sa ake samun matsalar dumamar yanayi, saboda haka, ko da wata kasa dake fama da koma bayan tattalin arziki a nahiyar Afirka, wadda ke jin radadin bala’i daga Indallahi da sauyawar yanayin duniya ta haddasa, ya kamata ta dauki nauyi na tinkarar matsalar sauyawar yanayin da kan ta. Kana kasashe masu sukuni ba sa bukatar biyan diyya ga kasashen masu tasowa.

To amma mene ne gaskiyar wannan batu? Sanin kowa ne, sannu a hankali, aikace-aikacen dan Adam na yin tasiri kan muhallin duiya. Tun kafin kasashe masu tasowa su fara raya masana’antunsu, kasashen yamma masu sukuni sun riga sun kwashe shekaru fiye da 200, suna kokarin bunkasa bangaren masana’antu, tare da fitar da dimbin iska mai dumama yanayi, da gurbata muhallin duniya sosai.

Hakan ya sa dukkan kasashe masu tasowa ke dauke da ra’ayin cewa, kamata ya yi, kasashe masu sukuni, da kasashe masu tasowa su dauki nauyi na bai daya, amma masu bambanci da juna, a yayin da ake tinkarar batun sauyawar yanayi.

Labarai Masu Nasaba

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

Wannan ra’ayi ya nuna adalci, da dacewa da al’adar mutanen duniya, ta sanya wanda ya gurbata muhalli biyan diyya.
Sai dai maganar Kerry ta saba wa wannan ra’ayi na bai daya na daukacin kasashe masu tasowa.

Lamarin da ya sanya ‘yan Afirka fushi sosai: Wasu kungiyoyin jama’a da yawa na kasashe fiye da 40 dake nahiyar Afirka, sun nuna takaicinsu, inda suka ce John Kerry ya yi wasan fatar baki ne kawai, kana ya halarci taron ne don neman janyo hankalin mutanen duniya kan huldar dake tsakanin Amurka da kasashen Afirka.

Hakika, zancen Kerry ya nuna yadda kasar Amurka, da sauran kasashen yamma suke da girman kai.

A ganinsu, yadda kasashe masu tasowa suke tsayawa kan samun adalci, wani yunkuri ne na neman kudi kawai.
Ban da wannan kuma, Kerry ya yi gargadi ga kasashen Afirka, cewa kar su zuba kudi da yawa a aikin hakar iskar gas, duk da cewa akwai kasashen Afirka da yawa da suke kokarin raya bangaren iskar gas, don tabbatar da tsaron makamashi. A cewar John Kerry, ya kamata a raya makamashi da ake sabuntawa, maimakon iskar gas. Ya ce, “kar ku maimaita kurakuran da muka yi a baya.” Nufinsa shi ne, saboda kasashen yamma sun taba yin kurakurai, don haka a yanzu sun fi sanin hanya mai dacewa da ya kamata a bi ta.

Ya kamata kasashen Afirka da sauran kasashe masu tasowa su bi umarnin kasashen yamma. A nan an nuna girman kai matuka.

Ta hanyar sauraron maganar John Kerry, za mu gane cewa, aikin tinkarar sauyawar yanayi ba shi da sauki. Kuma ba za a cimma nasara ba, sai dai in kasashen yamma daina nuna girman kai da son kai, sa’an nan su yi cudanya da kasashe masu tasowa cikin daidaito. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Ku Da Damar Cewa Uffan Idan DanSanda Sanye Da Kayan Aiki Ya Zabga Muku Mari —’Yansanda

Next Post

Xi Da Takwaransa Na Togo Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu

Related

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya
Daga Birnin Sin

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

3 hours ago
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

5 hours ago
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

6 hours ago
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

7 hours ago
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

1 day ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

1 day ago
Next Post
Xi Da Takwaransa Na Togo Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu

Xi Da Takwaransa Na Togo Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.