ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kalaman John Kerry Sun Nuna Girman Kai Na Kasashen Yamma

by CMG Hausa
4 years ago
Kerry

Kalaman da manzon musamman na shugaban kasar Amurka mai kula da aikin tinkarar sauyawar yanayi John Kerry ya furta, a taron ministocin kasashen Afirka kan aikin kare muhalli, wanda ya gudana a kasar Senegal a kwanan baya, sun ba ni mamaki sosai.

Saboda a gaban wakilan dukkan kasashen Afirka, mista Kerry ya ce kasashe masu sukuni, ba su da wani nauyi na tarihi game da batun sauyawar yanayin duniya.

  • Buhari Zai Yi Balaguro Zuwa Kasar Amurka Gobe Lahadi

A ganinsa, aikace-aikace na daukacin dan Adam ne ke sa ake samun matsalar dumamar yanayi, saboda haka, ko da wata kasa dake fama da koma bayan tattalin arziki a nahiyar Afirka, wadda ke jin radadin bala’i daga Indallahi da sauyawar yanayin duniya ta haddasa, ya kamata ta dauki nauyi na tinkarar matsalar sauyawar yanayin da kan ta. Kana kasashe masu sukuni ba sa bukatar biyan diyya ga kasashen masu tasowa.

ADVERTISEMENT

To amma mene ne gaskiyar wannan batu? Sanin kowa ne, sannu a hankali, aikace-aikacen dan Adam na yin tasiri kan muhallin duiya. Tun kafin kasashe masu tasowa su fara raya masana’antunsu, kasashen yamma masu sukuni sun riga sun kwashe shekaru fiye da 200, suna kokarin bunkasa bangaren masana’antu, tare da fitar da dimbin iska mai dumama yanayi, da gurbata muhallin duniya sosai.

Hakan ya sa dukkan kasashe masu tasowa ke dauke da ra’ayin cewa, kamata ya yi, kasashe masu sukuni, da kasashe masu tasowa su dauki nauyi na bai daya, amma masu bambanci da juna, a yayin da ake tinkarar batun sauyawar yanayi.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Wannan ra’ayi ya nuna adalci, da dacewa da al’adar mutanen duniya, ta sanya wanda ya gurbata muhalli biyan diyya.
Sai dai maganar Kerry ta saba wa wannan ra’ayi na bai daya na daukacin kasashe masu tasowa.

Lamarin da ya sanya ‘yan Afirka fushi sosai: Wasu kungiyoyin jama’a da yawa na kasashe fiye da 40 dake nahiyar Afirka, sun nuna takaicinsu, inda suka ce John Kerry ya yi wasan fatar baki ne kawai, kana ya halarci taron ne don neman janyo hankalin mutanen duniya kan huldar dake tsakanin Amurka da kasashen Afirka.

Hakika, zancen Kerry ya nuna yadda kasar Amurka, da sauran kasashen yamma suke da girman kai.

A ganinsu, yadda kasashe masu tasowa suke tsayawa kan samun adalci, wani yunkuri ne na neman kudi kawai.
Ban da wannan kuma, Kerry ya yi gargadi ga kasashen Afirka, cewa kar su zuba kudi da yawa a aikin hakar iskar gas, duk da cewa akwai kasashen Afirka da yawa da suke kokarin raya bangaren iskar gas, don tabbatar da tsaron makamashi. A cewar John Kerry, ya kamata a raya makamashi da ake sabuntawa, maimakon iskar gas. Ya ce, “kar ku maimaita kurakuran da muka yi a baya.” Nufinsa shi ne, saboda kasashen yamma sun taba yin kurakurai, don haka a yanzu sun fi sanin hanya mai dacewa da ya kamata a bi ta.

Ya kamata kasashen Afirka da sauran kasashe masu tasowa su bi umarnin kasashen yamma. A nan an nuna girman kai matuka.

Ta hanyar sauraron maganar John Kerry, za mu gane cewa, aikin tinkarar sauyawar yanayi ba shi da sauki. Kuma ba za a cimma nasara ba, sai dai in kasashen yamma daina nuna girman kai da son kai, sa’an nan su yi cudanya da kasashe masu tasowa cikin daidaito. (Bello Wang)

Kerry
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Xi Da Takwaransa Na Togo Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu

Xi Da Takwaransa Na Togo Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.