ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kalaman John Kerry Sun Nuna Girman Kai Na Kasashen Yamma

by CMG Hausa
4 years ago
Kerry

Kalaman da manzon musamman na shugaban kasar Amurka mai kula da aikin tinkarar sauyawar yanayi John Kerry ya furta, a taron ministocin kasashen Afirka kan aikin kare muhalli, wanda ya gudana a kasar Senegal a kwanan baya, sun ba ni mamaki sosai.

Saboda a gaban wakilan dukkan kasashen Afirka, mista Kerry ya ce kasashe masu sukuni, ba su da wani nauyi na tarihi game da batun sauyawar yanayin duniya.

  • Buhari Zai Yi Balaguro Zuwa Kasar Amurka Gobe Lahadi

A ganinsa, aikace-aikace na daukacin dan Adam ne ke sa ake samun matsalar dumamar yanayi, saboda haka, ko da wata kasa dake fama da koma bayan tattalin arziki a nahiyar Afirka, wadda ke jin radadin bala’i daga Indallahi da sauyawar yanayin duniya ta haddasa, ya kamata ta dauki nauyi na tinkarar matsalar sauyawar yanayin da kan ta. Kana kasashe masu sukuni ba sa bukatar biyan diyya ga kasashen masu tasowa.

ADVERTISEMENT

To amma mene ne gaskiyar wannan batu? Sanin kowa ne, sannu a hankali, aikace-aikacen dan Adam na yin tasiri kan muhallin duiya. Tun kafin kasashe masu tasowa su fara raya masana’antunsu, kasashen yamma masu sukuni sun riga sun kwashe shekaru fiye da 200, suna kokarin bunkasa bangaren masana’antu, tare da fitar da dimbin iska mai dumama yanayi, da gurbata muhallin duniya sosai.

Hakan ya sa dukkan kasashe masu tasowa ke dauke da ra’ayin cewa, kamata ya yi, kasashe masu sukuni, da kasashe masu tasowa su dauki nauyi na bai daya, amma masu bambanci da juna, a yayin da ake tinkarar batun sauyawar yanayi.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Wannan ra’ayi ya nuna adalci, da dacewa da al’adar mutanen duniya, ta sanya wanda ya gurbata muhalli biyan diyya.
Sai dai maganar Kerry ta saba wa wannan ra’ayi na bai daya na daukacin kasashe masu tasowa.

Lamarin da ya sanya ‘yan Afirka fushi sosai: Wasu kungiyoyin jama’a da yawa na kasashe fiye da 40 dake nahiyar Afirka, sun nuna takaicinsu, inda suka ce John Kerry ya yi wasan fatar baki ne kawai, kana ya halarci taron ne don neman janyo hankalin mutanen duniya kan huldar dake tsakanin Amurka da kasashen Afirka.

Hakika, zancen Kerry ya nuna yadda kasar Amurka, da sauran kasashen yamma suke da girman kai.

A ganinsu, yadda kasashe masu tasowa suke tsayawa kan samun adalci, wani yunkuri ne na neman kudi kawai.
Ban da wannan kuma, Kerry ya yi gargadi ga kasashen Afirka, cewa kar su zuba kudi da yawa a aikin hakar iskar gas, duk da cewa akwai kasashen Afirka da yawa da suke kokarin raya bangaren iskar gas, don tabbatar da tsaron makamashi. A cewar John Kerry, ya kamata a raya makamashi da ake sabuntawa, maimakon iskar gas. Ya ce, “kar ku maimaita kurakuran da muka yi a baya.” Nufinsa shi ne, saboda kasashen yamma sun taba yin kurakurai, don haka a yanzu sun fi sanin hanya mai dacewa da ya kamata a bi ta.

Ya kamata kasashen Afirka da sauran kasashe masu tasowa su bi umarnin kasashen yamma. A nan an nuna girman kai matuka.

Ta hanyar sauraron maganar John Kerry, za mu gane cewa, aikin tinkarar sauyawar yanayi ba shi da sauki. Kuma ba za a cimma nasara ba, sai dai in kasashen yamma daina nuna girman kai da son kai, sa’an nan su yi cudanya da kasashe masu tasowa cikin daidaito. (Bello Wang)

Kerry
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Next Post
Xi Da Takwaransa Na Togo Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu

Xi Da Takwaransa Na Togo Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.