• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamfanoni 5 Da Ake Sa Ran Za Su Kara Bunkasa A 2024

by Bello Hamza
1 year ago
in Tattalin Arziki
0
Kamfanoni 5 Da Ake Sa Ran Za Su Kara Bunkasa A 2024
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An fuskanci fadi-tashi a fannin tattalin arziki a shekarar 2023, masana na da ra’ayin cewa, in har ana son a sake yi wa tattalin arzikin Nijeriya alkibla dole a sake fasalin tafiyar da tattalin arzikin kasar ta hanyar karfafa masana’antunmu a kuma rage dogaro ga kayayyakin da ake sarrafawa a kasashen waje wannan ne zai bunkasa tare da daukaka darajar Naira a kasuewannin duniya.

Masanann sun yi hasashen kamfanonin da za su tabuka abin arziki a cikin wannan shekarar ta 2024, kamfanonin sun kuma hada da.

 

Matatar Mai Ta Dangote

All’ummar Nijeraiya sun yi murnar da fara aikin matatar man Daangote a da aka kashe fiye da Dala biliyan 19 wajen kafawa, wannan kuma a bayyane yake ganin irin halin matsin da aka shiga sakamakon cire tallafin mai da gwamnantin Bola Tinubu ta yi.

Labarai Masu Nasaba

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

Kwanaki ne kamfanin ya bayyana cewa, ya karbi danyen mai sampurin Agbami ta hannun kamfanonin MT ALMI wanda hakan ya taimaka musu gama shirye-shiryen fara aikin gwaji. Ana sa ran matatar man za ta tace gangan mai 650,000 wanda hakan zai rage dogaro da Nijeriya take yi da tataccen mai daga kasashen waje, fara aikin matatar mai na Dangote zai samar da ayyukan yi ga dimbin matasanmu zai kuma bayar da gaggaurumar gudummawa ga tattalin arzikin Nijeriya.

 

Kamfanin Siminti Na BUA

Kamfanin siminti na BUA zai fara sarrafa siminti tan miliyan 6 kari akan abin da yake sarrafawa a baya, tabbas wannan zai samar da gaggarumin canji ga tattalin arzkin kasa a shekarar 2024, musamman ganin hakan na nufin karin ma’aikata da kuma karin kudin shiga ga kamfanin.

Shugaban kamfani siminti na BUA, Abdul Samad Rabiu, ya ce wannan karin da kamfanin ya yi zai taimaka wajen samar da isassshen siminti a Nijeriya dama sassan nahiyar Afirka.

 

May & Baker

Wannan kamfanin hada magungunan ya yi alkawarin kaddamar da sabbin kayayyaki har guda 7 a wannan sabuwar shekarar ta 2024.

Tabbas kamfanin ‘May & Baker Nigeria’ na daya daga cikin kamfanonin da za su tabuka abin arziki a shekarar 2024 musamman ganin akwia gibi mai girma da za su cika bayan ficewar kamfanin hada magunguna na GSK a shekarar 2023.

Bayani ya nuna yadda fasahin magunguna suka yi tashin gwauron zabi bayan ficewar kamfanin GSK abin kuma da zai dora nauyin a kan kamfanin na May & Baker.

 

Seplat ANOH Gas

Ana sa ran wannan kamfanin zai rage yadda Nijeriya ke barnatar da iskar gas ya kuma taimaka wajen samar da issashen iskar gas a kasuwannin Nijeriya.

Kamfanin gas na ANOH hadaka ce tsakanin ta da kamfanin mai na NNPCL sun kuma samar da karkkarfar kamfanin da zai yi gogayya wajen cin kasuwar samar da iskar gas a fadin tarayyar Nijeriya.

 

Matatun Mai Na Fatakwal, Warri da Kaduna

A nasa ran matatun mai 4 da ke Nijeriya su fara aiki a cikin shekarar 2024, a halin yanzu matatar mai na Fatakwal ya fara aiki a watan Janairu.

Tun a shekarar 2022 aka shirya matatar mai na Fatakwal zai fara aiki amma saboda rashin kammala yi wa matatar garambawul lamarin ya kai zuwa yanzu.

Idan matatun man suka fara aiki yadda ya kamata, Nijeriya na fatan kawo karshen shigo da tataccen man fetur da dangoginsu daga kasashen waje, wanda haka zai karfafa tare da bunkasa tattalihn arzikin kasa

 

Kamfanin Mai Na A A Rano

Kamfanion mai na AA Rano ya yi fice a harkar samar da man fetur da dangoginsu. Shugaban Kamfanin, Alhaji Awwalu Rano haifaffen Jihar Kano ya kafa kamfanin ne a shekarar 1996 ya kuma zama cikakken kamfani a shekarar 2002. Kamfanin na da fiye da manyan motocin dakon fetur 600 yana kuma da gidajen mai fiye 115 a fadin kasar nan.

Haka kuma kamfanin ya shiga harkar zirga-zirgar jiragen sama in da a halin yanzu suke zirga-zirga a tsakanin garuruwan Abuja, Kano, Legas, Sokoto, Maiduguri, Kaduna, Yola da Asaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bunkasar tattalin arzikin NijeriyaHaramtacciyar matatar man feturKamfanin BUA
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Gabatar Da Taswirar Raya Kauyuka Cikin Takarda Mai Lamba 1 Ta Kwamitin Tsakiya Ta 2024

Next Post

INEC Ta Dakatar Da Sake Zabe A Kano, Enugu, Akwa Ibom Sakamakon Ayyukan ‘Yan Daba

Related

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

1 week ago
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

2 weeks ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

1 month ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

1 month ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA

1 month ago
Next Post
INEC Ta Dakatar Da Sake Zabe A Kano, Enugu, Akwa Ibom Sakamakon Ayyukan ‘Yan Daba

INEC Ta Dakatar Da Sake Zabe A Kano, Enugu, Akwa Ibom Sakamakon Ayyukan 'Yan Daba

LABARAI MASU NASABA

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Kamfanoni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.