ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamfanoni 5 Da Ake Sa Ran Za Su Kara Bunkasa A 2024

by Bello Hamza
2 years ago
Kamfanoni

An fuskanci fadi-tashi a fannin tattalin arziki a shekarar 2023, masana na da ra’ayin cewa, in har ana son a sake yi wa tattalin arzikin Nijeriya alkibla dole a sake fasalin tafiyar da tattalin arzikin kasar ta hanyar karfafa masana’antunmu a kuma rage dogaro ga kayayyakin da ake sarrafawa a kasashen waje wannan ne zai bunkasa tare da daukaka darajar Naira a kasuewannin duniya.

Masanann sun yi hasashen kamfanonin da za su tabuka abin arziki a cikin wannan shekarar ta 2024, kamfanonin sun kuma hada da.

 

ADVERTISEMENT

Matatar Mai Ta Dangote

All’ummar Nijeraiya sun yi murnar da fara aikin matatar man Daangote a da aka kashe fiye da Dala biliyan 19 wajen kafawa, wannan kuma a bayyane yake ganin irin halin matsin da aka shiga sakamakon cire tallafin mai da gwamnantin Bola Tinubu ta yi.

LABARAI MASU NASABA

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

Kwanaki ne kamfanin ya bayyana cewa, ya karbi danyen mai sampurin Agbami ta hannun kamfanonin MT ALMI wanda hakan ya taimaka musu gama shirye-shiryen fara aikin gwaji. Ana sa ran matatar man za ta tace gangan mai 650,000 wanda hakan zai rage dogaro da Nijeriya take yi da tataccen mai daga kasashen waje, fara aikin matatar mai na Dangote zai samar da ayyukan yi ga dimbin matasanmu zai kuma bayar da gaggaurumar gudummawa ga tattalin arzikin Nijeriya.

 

Kamfanin Siminti Na BUA

Kamfanin siminti na BUA zai fara sarrafa siminti tan miliyan 6 kari akan abin da yake sarrafawa a baya, tabbas wannan zai samar da gaggarumin canji ga tattalin arzkin kasa a shekarar 2024, musamman ganin hakan na nufin karin ma’aikata da kuma karin kudin shiga ga kamfanin.

Shugaban kamfani siminti na BUA, Abdul Samad Rabiu, ya ce wannan karin da kamfanin ya yi zai taimaka wajen samar da isassshen siminti a Nijeriya dama sassan nahiyar Afirka.

 

May & Baker

Wannan kamfanin hada magungunan ya yi alkawarin kaddamar da sabbin kayayyaki har guda 7 a wannan sabuwar shekarar ta 2024.

Tabbas kamfanin ‘May & Baker Nigeria’ na daya daga cikin kamfanonin da za su tabuka abin arziki a shekarar 2024 musamman ganin akwia gibi mai girma da za su cika bayan ficewar kamfanin hada magunguna na GSK a shekarar 2023.

Bayani ya nuna yadda fasahin magunguna suka yi tashin gwauron zabi bayan ficewar kamfanin GSK abin kuma da zai dora nauyin a kan kamfanin na May & Baker.

 

Seplat ANOH Gas

Ana sa ran wannan kamfanin zai rage yadda Nijeriya ke barnatar da iskar gas ya kuma taimaka wajen samar da issashen iskar gas a kasuwannin Nijeriya.

Kamfanin gas na ANOH hadaka ce tsakanin ta da kamfanin mai na NNPCL sun kuma samar da karkkarfar kamfanin da zai yi gogayya wajen cin kasuwar samar da iskar gas a fadin tarayyar Nijeriya.

 

Matatun Mai Na Fatakwal, Warri da Kaduna

A nasa ran matatun mai 4 da ke Nijeriya su fara aiki a cikin shekarar 2024, a halin yanzu matatar mai na Fatakwal ya fara aiki a watan Janairu.

Tun a shekarar 2022 aka shirya matatar mai na Fatakwal zai fara aiki amma saboda rashin kammala yi wa matatar garambawul lamarin ya kai zuwa yanzu.

Idan matatun man suka fara aiki yadda ya kamata, Nijeriya na fatan kawo karshen shigo da tataccen man fetur da dangoginsu daga kasashen waje, wanda haka zai karfafa tare da bunkasa tattalihn arzikin kasa

 

Kamfanin Mai Na A A Rano

Kamfanion mai na AA Rano ya yi fice a harkar samar da man fetur da dangoginsu. Shugaban Kamfanin, Alhaji Awwalu Rano haifaffen Jihar Kano ya kafa kamfanin ne a shekarar 1996 ya kuma zama cikakken kamfani a shekarar 2002. Kamfanin na da fiye da manyan motocin dakon fetur 600 yana kuma da gidajen mai fiye 115 a fadin kasar nan.

Haka kuma kamfanin ya shiga harkar zirga-zirgar jiragen sama in da a halin yanzu suke zirga-zirga a tsakanin garuruwan Abuja, Kano, Legas, Sokoto, Maiduguri, Kaduna, Yola da Asaba.

Kamfanoni
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tattalin Arziki

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Next Post
INEC Ta Dakatar Da Sake Zabe A Kano, Enugu, Akwa Ibom Sakamakon Ayyukan ‘Yan Daba

INEC Ta Dakatar Da Sake Zabe A Kano, Enugu, Akwa Ibom Sakamakon Ayyukan 'Yan Daba

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.