ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamfanoni 5 Da Ake Sa Ran Za Su Kara Bunkasa A 2024

by Bello Hamza
2 years ago
Kamfanoni

An fuskanci fadi-tashi a fannin tattalin arziki a shekarar 2023, masana na da ra’ayin cewa, in har ana son a sake yi wa tattalin arzikin Nijeriya alkibla dole a sake fasalin tafiyar da tattalin arzikin kasar ta hanyar karfafa masana’antunmu a kuma rage dogaro ga kayayyakin da ake sarrafawa a kasashen waje wannan ne zai bunkasa tare da daukaka darajar Naira a kasuewannin duniya.

Masanann sun yi hasashen kamfanonin da za su tabuka abin arziki a cikin wannan shekarar ta 2024, kamfanonin sun kuma hada da.

 

ADVERTISEMENT

Matatar Mai Ta Dangote

All’ummar Nijeraiya sun yi murnar da fara aikin matatar man Daangote a da aka kashe fiye da Dala biliyan 19 wajen kafawa, wannan kuma a bayyane yake ganin irin halin matsin da aka shiga sakamakon cire tallafin mai da gwamnantin Bola Tinubu ta yi.

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

Kwanaki ne kamfanin ya bayyana cewa, ya karbi danyen mai sampurin Agbami ta hannun kamfanonin MT ALMI wanda hakan ya taimaka musu gama shirye-shiryen fara aikin gwaji. Ana sa ran matatar man za ta tace gangan mai 650,000 wanda hakan zai rage dogaro da Nijeriya take yi da tataccen mai daga kasashen waje, fara aikin matatar mai na Dangote zai samar da ayyukan yi ga dimbin matasanmu zai kuma bayar da gaggaurumar gudummawa ga tattalin arzikin Nijeriya.

 

Kamfanin Siminti Na BUA

Kamfanin siminti na BUA zai fara sarrafa siminti tan miliyan 6 kari akan abin da yake sarrafawa a baya, tabbas wannan zai samar da gaggarumin canji ga tattalin arzkin kasa a shekarar 2024, musamman ganin hakan na nufin karin ma’aikata da kuma karin kudin shiga ga kamfanin.

Shugaban kamfani siminti na BUA, Abdul Samad Rabiu, ya ce wannan karin da kamfanin ya yi zai taimaka wajen samar da isassshen siminti a Nijeriya dama sassan nahiyar Afirka.

 

May & Baker

Wannan kamfanin hada magungunan ya yi alkawarin kaddamar da sabbin kayayyaki har guda 7 a wannan sabuwar shekarar ta 2024.

Tabbas kamfanin ‘May & Baker Nigeria’ na daya daga cikin kamfanonin da za su tabuka abin arziki a shekarar 2024 musamman ganin akwia gibi mai girma da za su cika bayan ficewar kamfanin hada magunguna na GSK a shekarar 2023.

Bayani ya nuna yadda fasahin magunguna suka yi tashin gwauron zabi bayan ficewar kamfanin GSK abin kuma da zai dora nauyin a kan kamfanin na May & Baker.

 

Seplat ANOH Gas

Ana sa ran wannan kamfanin zai rage yadda Nijeriya ke barnatar da iskar gas ya kuma taimaka wajen samar da issashen iskar gas a kasuwannin Nijeriya.

Kamfanin gas na ANOH hadaka ce tsakanin ta da kamfanin mai na NNPCL sun kuma samar da karkkarfar kamfanin da zai yi gogayya wajen cin kasuwar samar da iskar gas a fadin tarayyar Nijeriya.

 

Matatun Mai Na Fatakwal, Warri da Kaduna

A nasa ran matatun mai 4 da ke Nijeriya su fara aiki a cikin shekarar 2024, a halin yanzu matatar mai na Fatakwal ya fara aiki a watan Janairu.

Tun a shekarar 2022 aka shirya matatar mai na Fatakwal zai fara aiki amma saboda rashin kammala yi wa matatar garambawul lamarin ya kai zuwa yanzu.

Idan matatun man suka fara aiki yadda ya kamata, Nijeriya na fatan kawo karshen shigo da tataccen man fetur da dangoginsu daga kasashen waje, wanda haka zai karfafa tare da bunkasa tattalihn arzikin kasa

 

Kamfanin Mai Na A A Rano

Kamfanion mai na AA Rano ya yi fice a harkar samar da man fetur da dangoginsu. Shugaban Kamfanin, Alhaji Awwalu Rano haifaffen Jihar Kano ya kafa kamfanin ne a shekarar 1996 ya kuma zama cikakken kamfani a shekarar 2002. Kamfanin na da fiye da manyan motocin dakon fetur 600 yana kuma da gidajen mai fiye 115 a fadin kasar nan.

Haka kuma kamfanin ya shiga harkar zirga-zirgar jiragen sama in da a halin yanzu suke zirga-zirga a tsakanin garuruwan Abuja, Kano, Legas, Sokoto, Maiduguri, Kaduna, Yola da Asaba.

Kamfanoni
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Next Post
INEC Ta Dakatar Da Sake Zabe A Kano, Enugu, Akwa Ibom Sakamakon Ayyukan ‘Yan Daba

INEC Ta Dakatar Da Sake Zabe A Kano, Enugu, Akwa Ibom Sakamakon Ayyukan 'Yan Daba

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.