ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamfanoni 5 Da Ake Sa Ran Za Su Kara Bunkasa A 2024

by Bello Hamza
3 years ago
Kamfanoni

An fuskanci fadi-tashi a fannin tattalin arziki a shekarar 2023, masana na da ra’ayin cewa, in har ana son a sake yi wa tattalin arzikin Nijeriya alkibla dole a sake fasalin tafiyar da tattalin arzikin kasar ta hanyar karfafa masana’antunmu a kuma rage dogaro ga kayayyakin da ake sarrafawa a kasashen waje wannan ne zai bunkasa tare da daukaka darajar Naira a kasuewannin duniya.

Masanann sun yi hasashen kamfanonin da za su tabuka abin arziki a cikin wannan shekarar ta 2024, kamfanonin sun kuma hada da.

 

ADVERTISEMENT

Matatar Mai Ta Dangote

All’ummar Nijeraiya sun yi murnar da fara aikin matatar man Daangote a da aka kashe fiye da Dala biliyan 19 wajen kafawa, wannan kuma a bayyane yake ganin irin halin matsin da aka shiga sakamakon cire tallafin mai da gwamnantin Bola Tinubu ta yi.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

Kwanaki ne kamfanin ya bayyana cewa, ya karbi danyen mai sampurin Agbami ta hannun kamfanonin MT ALMI wanda hakan ya taimaka musu gama shirye-shiryen fara aikin gwaji. Ana sa ran matatar man za ta tace gangan mai 650,000 wanda hakan zai rage dogaro da Nijeriya take yi da tataccen mai daga kasashen waje, fara aikin matatar mai na Dangote zai samar da ayyukan yi ga dimbin matasanmu zai kuma bayar da gaggaurumar gudummawa ga tattalin arzikin Nijeriya.

 

Kamfanin Siminti Na BUA

Kamfanin siminti na BUA zai fara sarrafa siminti tan miliyan 6 kari akan abin da yake sarrafawa a baya, tabbas wannan zai samar da gaggarumin canji ga tattalin arzkin kasa a shekarar 2024, musamman ganin hakan na nufin karin ma’aikata da kuma karin kudin shiga ga kamfanin.

Shugaban kamfani siminti na BUA, Abdul Samad Rabiu, ya ce wannan karin da kamfanin ya yi zai taimaka wajen samar da isassshen siminti a Nijeriya dama sassan nahiyar Afirka.

 

May & Baker

Wannan kamfanin hada magungunan ya yi alkawarin kaddamar da sabbin kayayyaki har guda 7 a wannan sabuwar shekarar ta 2024.

Tabbas kamfanin ‘May & Baker Nigeria’ na daya daga cikin kamfanonin da za su tabuka abin arziki a shekarar 2024 musamman ganin akwia gibi mai girma da za su cika bayan ficewar kamfanin hada magunguna na GSK a shekarar 2023.

Bayani ya nuna yadda fasahin magunguna suka yi tashin gwauron zabi bayan ficewar kamfanin GSK abin kuma da zai dora nauyin a kan kamfanin na May & Baker.

 

Seplat ANOH Gas

Ana sa ran wannan kamfanin zai rage yadda Nijeriya ke barnatar da iskar gas ya kuma taimaka wajen samar da issashen iskar gas a kasuwannin Nijeriya.

Kamfanin gas na ANOH hadaka ce tsakanin ta da kamfanin mai na NNPCL sun kuma samar da karkkarfar kamfanin da zai yi gogayya wajen cin kasuwar samar da iskar gas a fadin tarayyar Nijeriya.

 

Matatun Mai Na Fatakwal, Warri da Kaduna

A nasa ran matatun mai 4 da ke Nijeriya su fara aiki a cikin shekarar 2024, a halin yanzu matatar mai na Fatakwal ya fara aiki a watan Janairu.

Tun a shekarar 2022 aka shirya matatar mai na Fatakwal zai fara aiki amma saboda rashin kammala yi wa matatar garambawul lamarin ya kai zuwa yanzu.

Idan matatun man suka fara aiki yadda ya kamata, Nijeriya na fatan kawo karshen shigo da tataccen man fetur da dangoginsu daga kasashen waje, wanda haka zai karfafa tare da bunkasa tattalihn arzikin kasa

 

Kamfanin Mai Na A A Rano

Kamfanion mai na AA Rano ya yi fice a harkar samar da man fetur da dangoginsu. Shugaban Kamfanin, Alhaji Awwalu Rano haifaffen Jihar Kano ya kafa kamfanin ne a shekarar 1996 ya kuma zama cikakken kamfani a shekarar 2002. Kamfanin na da fiye da manyan motocin dakon fetur 600 yana kuma da gidajen mai fiye 115 a fadin kasar nan.

Haka kuma kamfanin ya shiga harkar zirga-zirgar jiragen sama in da a halin yanzu suke zirga-zirga a tsakanin garuruwan Abuja, Kano, Legas, Sokoto, Maiduguri, Kaduna, Yola da Asaba.

Kamfanoni
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Abin Da Ya Kamata Ka Sani Kan Hannun Jarin Matatar Dangote
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa

MASU ALAKA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas
Tattalin Arziki

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

September 4, 2026
NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
Tattalin Arziki

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

September 4, 2026
NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja
Tattalin Arziki

NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja

August 28, 2026
Next Post
INEC Ta Dakatar Da Sake Zabe A Kano, Enugu, Akwa Ibom Sakamakon Ayyukan ‘Yan Daba

INEC Ta Dakatar Da Sake Zabe A Kano, Enugu, Akwa Ibom Sakamakon Ayyukan 'Yan Daba

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

September 11, 2026
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026  Mrs Zubaida Umar

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026 Mrs Zubaida Umar

September 11, 2026
Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

September 11, 2026
Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

September 11, 2026
Sanata yari

Gwarzon Ɗan Siyasa Na Shekarar 2026 Sanata Abdul’Aziz Abubakar Yari

September 11, 2026
Kasar Sin Za Ta Taimaka Wajen Bunkasa Wadatar Makamashi Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Za Ta Taimaka Wajen Bunkasa Wadatar Makamashi Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 11, 2026
SAW

Ɗabi’un Annabi (SAW) Kan Abubuwa Na Al’adar Rayuwa

September 11, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Horar Da Malamai 250,000

Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Horar Da Malamai 250,000

September 11, 2026
Kamfanoni

Sojoji Sun Ceto Mutane 13 Da ’Yan Bindiga Suka Yi Garkuwa Da Su

September 11, 2026
Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.