• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kananan Kamfanoni Miliyan 10 Suka Durkushe A Shekarar 2023 – ASBON

by Bello Hamza
1 year ago
in Tattalin Arziki
0
Kananan Kamfanoni Miliyan 10 Suka Durkushe A Shekarar 2023 – ASBON
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar masu Kananan Masana’antu ta Nijeriya (ASBON) ta bayyana cewa, fiye da kananan masana’antu miliyan 10 ne suka durkushe a shekarar da ta gabata 2023.

Shugaban kungiyar, Femi Egbesola, ya sanar da haka a tattunawarsa da manema labarai, ya ce, kamfanonin sun durkushe ne sakamakon matsalar tattalin arziki a Nijeriya.

  • Kwastam Ta Tara Biliyan 52.7 A Kano Da Jigawa A 2023
  • Kasashen Afirka Na Fadada Cudanya Da Kasar Sin A Fannoni Daban Daban

Janye tallafin man fetur da Shugaban Kasa Bola Tinubu ya yi a yayin rantsar da shi ranar 29 ga wata Mayu 2023 da kuma karin farashin man fetur da sauran kayan masarufi sun kara hauhawar farashin kayyakin amfanin yau da kullum wanda ya haifar da rashin aikin yi ga matasa wanda kuma ya kai ga karin talauci a tsakanin ‘yan Nijeriya.

Hukumar kididdiga ta kasa NBC ta bayyana cewa a watan Nuwamba na 2023 an samu hauhawar farashi na kashi 28.20 ba kamar yadda yake ba a watan Oktoba 2023 na kashi 27.33.

Da yake tsokaci a kan yadda matsin tattalin arzikki ya shafi mambobinsu, Egbesola ya bayyana cewa, “Kashi 25 na kamfanonin da ake da su suka mutu a shekarar 2023, wannan ne mafi yawa a tarihin mutuwar kamfanoni a kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

“A halin yanzu muna da kamfanoni miliyan 40 a kasar nan da bayanan su ke cikin kundin tattara bayanai, idan ka cire kashi 25, yana nuna kenan kamfanoni miliyan 10 suka mutu.

“A wasu kasashen in har aka samu irin haka, gwamnati na sanya dokar ta-baci ne a sashin don wadannan kanana kamfanoni sune ke rikida su zama manyan kamfanoni a nan gaba. Idan zaka kuma yi tambaya a cikin shekara 10 da suka wuce kananan kamfanoni nawa ne suka zama manyan kamfanoni? Lallai ba a abin a zo a gani ba ne”

Ya kuma kara da cewa, in har ana son ceto kananan kamfanoni daga durkushewa a cikin wannan sabuwar shekarar dole gwamnati ta tabbatar da gyara hanyoyi da kuma samar da wutar lantarki da kuma samar da bashi mara ruwa ga kananan kamfanoni don tabbatar da bunkasar su.

In har aka samar da wadannan tabbas kamfanoni da dama za su bunkasa, su kuma taimaka wajen daukar matasanmu aikin yi abin da kuma zai rage ayyuykan masu aikata laifukka a fadin tarayyar Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kananan masana'antuMSMETattalin Arziki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nokia Na Shirin Sallamar Ma’aikata 4,000

Next Post

Xi Jinping: Ya Kamata Daukar Nauyi Ya Zama Al’ada

Related

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

4 hours ago
Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

1 week ago
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

2 weeks ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

1 month ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

1 month ago
Next Post
Xi Jinping: Ya Kamata Daukar Nauyi Ya Zama Al’ada

Xi Jinping: Ya Kamata Daukar Nauyi Ya Zama Al'ada

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.