• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kananan Kamfanoni Miliyan 10 Suka Durkushe A Shekarar 2023 – ASBON

by Bello Hamza
2 years ago
ASBON

Kungiyar masu Kananan Masana’antu ta Nijeriya (ASBON) ta bayyana cewa, fiye da kananan masana’antu miliyan 10 ne suka durkushe a shekarar da ta gabata 2023.

Shugaban kungiyar, Femi Egbesola, ya sanar da haka a tattunawarsa da manema labarai, ya ce, kamfanonin sun durkushe ne sakamakon matsalar tattalin arziki a Nijeriya.

  • Kwastam Ta Tara Biliyan 52.7 A Kano Da Jigawa A 2023
  • Kasashen Afirka Na Fadada Cudanya Da Kasar Sin A Fannoni Daban Daban

Janye tallafin man fetur da Shugaban Kasa Bola Tinubu ya yi a yayin rantsar da shi ranar 29 ga wata Mayu 2023 da kuma karin farashin man fetur da sauran kayan masarufi sun kara hauhawar farashin kayyakin amfanin yau da kullum wanda ya haifar da rashin aikin yi ga matasa wanda kuma ya kai ga karin talauci a tsakanin ‘yan Nijeriya.

Hukumar kididdiga ta kasa NBC ta bayyana cewa a watan Nuwamba na 2023 an samu hauhawar farashi na kashi 28.20 ba kamar yadda yake ba a watan Oktoba 2023 na kashi 27.33.

Da yake tsokaci a kan yadda matsin tattalin arzikki ya shafi mambobinsu, Egbesola ya bayyana cewa, “Kashi 25 na kamfanonin da ake da su suka mutu a shekarar 2023, wannan ne mafi yawa a tarihin mutuwar kamfanoni a kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life

“A halin yanzu muna da kamfanoni miliyan 40 a kasar nan da bayanan su ke cikin kundin tattara bayanai, idan ka cire kashi 25, yana nuna kenan kamfanoni miliyan 10 suka mutu.

“A wasu kasashen in har aka samu irin haka, gwamnati na sanya dokar ta-baci ne a sashin don wadannan kanana kamfanoni sune ke rikida su zama manyan kamfanoni a nan gaba. Idan zaka kuma yi tambaya a cikin shekara 10 da suka wuce kananan kamfanoni nawa ne suka zama manyan kamfanoni? Lallai ba a abin a zo a gani ba ne”

Ya kuma kara da cewa, in har ana son ceto kananan kamfanoni daga durkushewa a cikin wannan sabuwar shekarar dole gwamnati ta tabbatar da gyara hanyoyi da kuma samar da wutar lantarki da kuma samar da bashi mara ruwa ga kananan kamfanoni don tabbatar da bunkasar su.

In har aka samar da wadannan tabbas kamfanoni da dama za su bunkasa, su kuma taimaka wajen daukar matasanmu aikin yi abin da kuma zai rage ayyuykan masu aikata laifukka a fadin tarayyar Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria
Tattalin Arziki

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

October 25, 2025
Tattalin Arziki

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life

October 25, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA
Tattalin Arziki

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Next Post
Xi Jinping: Ya Kamata Daukar Nauyi Ya Zama Al’ada

Xi Jinping: Ya Kamata Daukar Nauyi Ya Zama Al'ada

LABARAI MASU NASABA

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

November 2, 2025
Maganin Nankarwa (3)

Maganin Nankarwa (3)

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legas

November 2, 2025
Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

November 2, 2025
Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

November 2, 2025
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano

An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano

November 2, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.