• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kananan Kamfanoni Miliyan 10 Suka Durkushe A Shekarar 2023 – ASBON

by Bello Hamza
2 years ago
in Tattalin Arziki
0
Kananan Kamfanoni Miliyan 10 Suka Durkushe A Shekarar 2023 – ASBON
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar masu Kananan Masana’antu ta Nijeriya (ASBON) ta bayyana cewa, fiye da kananan masana’antu miliyan 10 ne suka durkushe a shekarar da ta gabata 2023.

Shugaban kungiyar, Femi Egbesola, ya sanar da haka a tattunawarsa da manema labarai, ya ce, kamfanonin sun durkushe ne sakamakon matsalar tattalin arziki a Nijeriya.

  • Kwastam Ta Tara Biliyan 52.7 A Kano Da Jigawa A 2023
  • Kasashen Afirka Na Fadada Cudanya Da Kasar Sin A Fannoni Daban Daban

Janye tallafin man fetur da Shugaban Kasa Bola Tinubu ya yi a yayin rantsar da shi ranar 29 ga wata Mayu 2023 da kuma karin farashin man fetur da sauran kayan masarufi sun kara hauhawar farashin kayyakin amfanin yau da kullum wanda ya haifar da rashin aikin yi ga matasa wanda kuma ya kai ga karin talauci a tsakanin ‘yan Nijeriya.

Hukumar kididdiga ta kasa NBC ta bayyana cewa a watan Nuwamba na 2023 an samu hauhawar farashi na kashi 28.20 ba kamar yadda yake ba a watan Oktoba 2023 na kashi 27.33.

Da yake tsokaci a kan yadda matsin tattalin arzikki ya shafi mambobinsu, Egbesola ya bayyana cewa, “Kashi 25 na kamfanonin da ake da su suka mutu a shekarar 2023, wannan ne mafi yawa a tarihin mutuwar kamfanoni a kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

“A halin yanzu muna da kamfanoni miliyan 40 a kasar nan da bayanan su ke cikin kundin tattara bayanai, idan ka cire kashi 25, yana nuna kenan kamfanoni miliyan 10 suka mutu.

“A wasu kasashen in har aka samu irin haka, gwamnati na sanya dokar ta-baci ne a sashin don wadannan kanana kamfanoni sune ke rikida su zama manyan kamfanoni a nan gaba. Idan zaka kuma yi tambaya a cikin shekara 10 da suka wuce kananan kamfanoni nawa ne suka zama manyan kamfanoni? Lallai ba a abin a zo a gani ba ne”

Ya kuma kara da cewa, in har ana son ceto kananan kamfanoni daga durkushewa a cikin wannan sabuwar shekarar dole gwamnati ta tabbatar da gyara hanyoyi da kuma samar da wutar lantarki da kuma samar da bashi mara ruwa ga kananan kamfanoni don tabbatar da bunkasar su.

In har aka samar da wadannan tabbas kamfanoni da dama za su bunkasa, su kuma taimaka wajen daukar matasanmu aikin yi abin da kuma zai rage ayyuykan masu aikata laifukka a fadin tarayyar Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kananan masana'antuMSMETattalin Arziki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nokia Na Shirin Sallamar Ma’aikata 4,000

Next Post

Xi Jinping: Ya Kamata Daukar Nauyi Ya Zama Al’ada

Related

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Tattalin Arziki

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

4 hours ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

1 week ago
tallafi
Tattalin Arziki

Kudaden Ajiya Na Asusun Nijeriya Ya Karu Zuwa Dala Biliyan 41

2 weeks ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

2 weeks ago
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5
Tattalin Arziki

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

2 weeks ago
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya
Tattalin Arziki

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

3 weeks ago
Next Post
Xi Jinping: Ya Kamata Daukar Nauyi Ya Zama Al’ada

Xi Jinping: Ya Kamata Daukar Nauyi Ya Zama Al'ada

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

September 14, 2025
Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

September 14, 2025
Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

September 14, 2025
An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

September 14, 2025
Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

September 14, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

September 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

September 14, 2025
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

September 14, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.