ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Afirka Na Fadada Cudanya Da Kasar Sin A Fannoni Daban Daban

by CGTN Hausa
2 years ago
Afirka

Ga duk mai bibiyar harkokin da suka shafi cudanyar kasar Sin da kasashen Afirka musamman a shekarar 2023 da ta gabata, ba zai rasa ganin muhimman nasarori da sassan biyu suka cimma a fannin yaukaka dangankata, da cimma moriya tare ba. 

Karkashin dandalin bunkasa hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka na FOCAC, da manufofin bunkasa ci gaban duniya, da na wanzar da tsaron kasa da kasa, da shawarar wayewar kan duniya, tare da karfafa matakan gina shawarar “ziri daya da hanya daya” ko BRI da Sin ta gabatar, an kai ga cimma manyan nasarori masu fa’idar gaske.

  • Xi Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Iran Bisa Munanan Hare-haren Ta’addanci Da Aka Kai A Kasar
  • Jarin Sin Ya Bunkasa Sashen Sabbin Makamashi A Zimbabwe

A baya-bayan nan, mun ga yadda hadin gwiwa tsakanin Sin da Habasha ke kara samun tagomashi a fannonin cinikayya, da zuba jari, da samar da manyan ababen more rayuwa, da noma da sadarwa. Sauran sun hada da fannin raya al’adu, da ilimi, da musaya tsakanin al’ummun sassan biyu da sauransu, wanda hakan ya haifar da moriya mai tarin yawa ga jama’ar kasashen biyu.

ADVERTISEMENT

A bana kuma, ana sa ran aiwatar da matakai daban daban na daga matsayin dangantakar Sin da Habasha bisa mutunta juna, da fadada tattaunawa tsakanin jami’ai, ta yadda za a gudu tare a tsira tare.

Baya ga Habasha, ita ma kasar Tunisiya ta karbi bakuncin taron musaya a fannin wayewar kai na hadin gwiwa da kasar Sin, taron da ya gudana a farkon makon jiya a birnin Tunis.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

An jiyo wasu daga manyan baki mahalarta taron na bayyana shi a matsayin dama ta musaya, da tattaunawa game da wayewar kan Sin da Tunisiya, wanda zai ingiza ci gaban bai daya, da wadata tsakanin kasashen biyu.

Kaza lika, wasu masharhanta na ganin shawarar Sin ta ingiza wayewar kan duniya, wadda ke fatan ganin an samu zaman jituwa da koyi daga nasarorin juna tsakanin wayewar kai daban daban, karkashin taruka masu kama da irin wanda aka shirya a birnin Tunis, zai taimaka matuka wajen bunkasa wayewar kan daukacin bil adama.

Yayin da Sin da Tunisiya ke samun karin tagomashi a fannin bunkasa dangantaka, da yadda Sin din ke fadada cudanya da Habasha, sauran kasashen Afirka ma na bin wannan tafarki, na cin gajiya, tare kasa mafi girma a jerin kasashe masu tasowa wato kasar Sin, musamman a shekarun baya bayan nan.

Fatan dai shi ne kamar yadda aka raya kyakkyawar dangantaka tsakanin kasashen Afirka da Sin a shekarar 2023 da ta shude, hakan zai dore a bana wato shekarar 2024, zuwa shekaru da dama a nan gaba, ta yadda tafiya tsakanin Sin da kawayenta kasashe masu tasowa za ta dore har abada. (Saminu Alhassan)

Afirka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Next Post
CMG Ya Gabatar Da Dandamali 4 Na Nuna Shirin Talibijin Na Murnar Sabuwar Shekarar 2024 Bisa Kalandar Gargajiyar Kasar Sin 

CMG Ya Gabatar Da Dandamali 4 Na Nuna Shirin Talibijin Na Murnar Sabuwar Shekarar 2024 Bisa Kalandar Gargajiyar Kasar Sin 

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.