ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Afirka Na Fadada Cudanya Da Kasar Sin A Fannoni Daban Daban

by CGTN Hausa
3 years ago
Afirka

Ga duk mai bibiyar harkokin da suka shafi cudanyar kasar Sin da kasashen Afirka musamman a shekarar 2023 da ta gabata, ba zai rasa ganin muhimman nasarori da sassan biyu suka cimma a fannin yaukaka dangankata, da cimma moriya tare ba. 

Karkashin dandalin bunkasa hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka na FOCAC, da manufofin bunkasa ci gaban duniya, da na wanzar da tsaron kasa da kasa, da shawarar wayewar kan duniya, tare da karfafa matakan gina shawarar “ziri daya da hanya daya” ko BRI da Sin ta gabatar, an kai ga cimma manyan nasarori masu fa’idar gaske.

  • Xi Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Iran Bisa Munanan Hare-haren Ta’addanci Da Aka Kai A Kasar
  • Jarin Sin Ya Bunkasa Sashen Sabbin Makamashi A Zimbabwe

A baya-bayan nan, mun ga yadda hadin gwiwa tsakanin Sin da Habasha ke kara samun tagomashi a fannonin cinikayya, da zuba jari, da samar da manyan ababen more rayuwa, da noma da sadarwa. Sauran sun hada da fannin raya al’adu, da ilimi, da musaya tsakanin al’ummun sassan biyu da sauransu, wanda hakan ya haifar da moriya mai tarin yawa ga jama’ar kasashen biyu.

ADVERTISEMENT

A bana kuma, ana sa ran aiwatar da matakai daban daban na daga matsayin dangantakar Sin da Habasha bisa mutunta juna, da fadada tattaunawa tsakanin jami’ai, ta yadda za a gudu tare a tsira tare.

Baya ga Habasha, ita ma kasar Tunisiya ta karbi bakuncin taron musaya a fannin wayewar kai na hadin gwiwa da kasar Sin, taron da ya gudana a farkon makon jiya a birnin Tunis.

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

An jiyo wasu daga manyan baki mahalarta taron na bayyana shi a matsayin dama ta musaya, da tattaunawa game da wayewar kan Sin da Tunisiya, wanda zai ingiza ci gaban bai daya, da wadata tsakanin kasashen biyu.

Kaza lika, wasu masharhanta na ganin shawarar Sin ta ingiza wayewar kan duniya, wadda ke fatan ganin an samu zaman jituwa da koyi daga nasarorin juna tsakanin wayewar kai daban daban, karkashin taruka masu kama da irin wanda aka shirya a birnin Tunis, zai taimaka matuka wajen bunkasa wayewar kan daukacin bil adama.

Yayin da Sin da Tunisiya ke samun karin tagomashi a fannin bunkasa dangantaka, da yadda Sin din ke fadada cudanya da Habasha, sauran kasashen Afirka ma na bin wannan tafarki, na cin gajiya, tare kasa mafi girma a jerin kasashe masu tasowa wato kasar Sin, musamman a shekarun baya bayan nan.

Fatan dai shi ne kamar yadda aka raya kyakkyawar dangantaka tsakanin kasashen Afirka da Sin a shekarar 2023 da ta shude, hakan zai dore a bana wato shekarar 2024, zuwa shekaru da dama a nan gaba, ta yadda tafiya tsakanin Sin da kawayenta kasashe masu tasowa za ta dore har abada. (Saminu Alhassan)

Afirka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

MASU ALAKA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
Next Post
CMG Ya Gabatar Da Dandamali 4 Na Nuna Shirin Talibijin Na Murnar Sabuwar Shekarar 2024 Bisa Kalandar Gargajiyar Kasar Sin 

CMG Ya Gabatar Da Dandamali 4 Na Nuna Shirin Talibijin Na Murnar Sabuwar Shekarar 2024 Bisa Kalandar Gargajiyar Kasar Sin 

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.