• Leadership Hausa
Saturday, January 28, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Da ɗumi-ɗuminsa

Karancin Man Fetur Da Sauya Kudade Shiri Ne Na Hana Zaben 2023 —Tinubu

by Sadiq
3 days ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
Karancin Man Fetur Da Sauya Kudade Shiri Ne Na Hana Zaben 2023 —Tinubu

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, ya ayyana matsalar karancin man fetur da kuma shirin sauya fasalin kudi da Babban Bankin Nijeriya (CBN), ya bullo da shi a matsayin wani shiri na kawo tsaiko ga zabe mai zuwa.

Tinubu ya bukaci ‘yan Nijeriya da kada su bari karancin man fetur ya sanyaya musu guiwa kan gudanar da ayyukansu na yau da kullum.

  • Ministan Harkokin Wajen Argentina: Sin Muhimmiyar Abokiyar Cinikayya Ce Ta Argentina
  • Xi Jinping Ya Gabatar Da Sakon Bidiyo Ga Taron Koli Karo Na 7 Na Kungiyar Kasashen Latin Amurka Da Caribbean

Tinubu ya bayyana karara cewa karancin man fetur da ake fama da shi tamkar zagon kasa ne sannan ya danganta lamarin da cewar da gangan na haddasa shi.

Dan takarar na APC ya bayyana haka ne a Abeokuta, yayin yakin neman zabensa a Jihar Ogun.

Yayin zargin cewar an hada baki da yin barna wajen samar da wutar lantarki, inda ya danganta sauya fasalin kudade da aka yi a matsayin wani shiri na dagula wa mutane lissafi.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Adeleke Ya Yi Watsi Da Hukuncin Kotu Da Ta Rushe Zabensa, Zai Daukaka Kara

Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Kori Adeleke A Matsayin Gwamnan Jihar Osun

“Ko sun ce babu mai a kasa, za mu yi tattaki don kada kuri’a. Sum yi barna da yawa don haka za su iya cewa, babu mai. Wannan zai iya haifar da rikici ta hanyar zagon kasa ga wadatar mai a kasa.

“Suna yin zagon kasa ga samar da mai. Ko man fetur ko babu za mu je mu kada kuri’a kuma za mu yi nasara. Wannan juyin juya hali ne mafi girma kuma idan na fada muku, kun san abin da nake nufi. Kun san ni ne zan sauya komai.

“Sun yi ta shirin haifar da matsalar mai, amma a manta da komai. Ni, Asiwaju zan magance matsalar samar da mai har abada.

“Ni dan gida ne, na zo nan, kuma ba zan ba ku kunya ba, za mu karbi mulki.

“Wannan juyin juya hali ne, wannan zabe juyin juya hali ne. Sun yin makirci, amma za su sha kasa. Sun ce farashin mai zai karu kuma zai kai Naira 200 kowace lita.Ba sa son a gudanar da wannan zabe, suna son a murde shi,” in ji Tinubu.

Da yake magana game da tsare-tsarensa ga matasan Nijeriya, Tinubu ya yi alkawarin bullo da shirin ba da lamuni ga dalibai, tare da samar da tsarin ilimi wanda zai magance matsalolin malamai da tabbatar da cewa dalibai sun kammala karatu a lokacin da ya dace.

“Ina ba ku tabbacin abu daya: zan bai wa dalibai lamuni. Babu wanda zai daina zuwa Jami’ar saboda kudin makaranta. Ina ba ku tabbacin cewa babu wanda zai sake maimaita shekaru ba tare da ya kammala karatunsa ba.”

Tags: APCCBNKarancin MaiSauya Fasalin NairaTinubuZabe
Previous Post

Ministan Harkokin Wajen Argentina: Sin Muhimmiyar Abokiyar Cinikayya Ce Ta Argentina

Next Post

Qin Gang Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Ma’aikatar Harkokin Wajen Gabon Bisa Rasuwar Ministan Harkokin Wajen Kasar Michael Moussa-Adamo

Related

Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Kori Adeleke A Matsayin Gwamnan Jihar Osun
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Adeleke Ya Yi Watsi Da Hukuncin Kotu Da Ta Rushe Zabensa, Zai Daukaka Kara

1 day ago
Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Kori Adeleke A Matsayin Gwamnan Jihar Osun
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Kori Adeleke A Matsayin Gwamnan Jihar Osun

1 day ago
Dan Gwamnan Jihar Nasarawa Mai Shekaru 36, Hassan Sule Ya Rasu
Da ɗumi-ɗuminsa

Dan Gwamnan Jihar Nasarawa Mai Shekaru 36, Hassan Sule Ya Rasu

2 days ago
Da Dumi-Dumi: Dan Takarar Gwamna Ya Rasu A Adamawa
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Dumi-Dumi: Dan Takarar Gwamna Ya Rasu A Adamawa

2 days ago
Da Dumi-Dumi: Dan Takarar Gwamnan Jihar Abia Na Jam’iyyar PDP Ya Rasu
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Dumi-Dumi: Dan Takarar Gwamnan Jihar Abia Na Jam’iyyar PDP Ya Rasu

3 days ago
Buhari Ya Kaddamar Da Aikin Tashar Jirgin Ruwa Ta Zamani Da Ke Lekki Jihar Legas
Da ɗumi-ɗuminsa

Buhari Ya Kaddamar Da Aikin Tashar Jirgin Ruwa Ta Zamani Da Ke Lekki Jihar Legas

5 days ago
Next Post
Qin Gang Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Ma’aikatar Harkokin Wajen Gabon Bisa Rasuwar Ministan Harkokin Wajen Kasar Michael Moussa-Adamo

Qin Gang Ya Aike Da Sakon Ta'aziyya Ga Ma'aikatar Harkokin Wajen Gabon Bisa Rasuwar Ministan Harkokin Wajen Kasar Michael Moussa-Adamo

LABARAI MASU NASABA

Tsokaci Kan Dukan Da Wasu Maza Ke Wa Matansu

Tsokaci Kan Dukan Da Wasu Maza Ke Wa Matansu

January 28, 2023
Babu Wata Baraka Tsakanina Da Buhari – Tinubu

Babu Wata Baraka Tsakanina Da Buhari – Tinubu

January 28, 2023
‘Yansanda Sun Kama Kasurguman ‘Yan Bindiga 2, Sun Ceto Mutane 7, Sun Kwato 2.1m Kudin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Kasurguman ‘Yan Bindiga 2, Sun Ceto Mutane 7, Sun Kwato 2.1m Kudin Fansa

January 28, 2023
Son Rai Da Rashin Cancantar Jarumai Ke Gurbata Al’adu A Fina-finanmu –Daushe

Son Rai Da Rashin Cancantar Jarumai Ke Gurbata Al’adu A Fina-finanmu –Daushe

January 28, 2023
Mataimakin Wakilin Kasar Sin Dake MDD Ya Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Taimakawa Mali Kara Karfin Yaki Da Ta’addanci

Mataimakin Wakilin Kasar Sin Dake MDD Ya Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Taimakawa Mali Kara Karfin Yaki Da Ta’addanci

January 28, 2023
Bikin Bazara Na Gargajiyar Kasar Sin Ya Kara Azama Kan Farfadowar Tattalin Arzikin Duniya

Bikin Bazara Na Gargajiyar Kasar Sin Ya Kara Azama Kan Farfadowar Tattalin Arzikin Duniya

January 28, 2023
Noman Kankana Na Kara Bunkasa A Jihar Jigawa

Noman Kankana Na Kara Bunkasa A Jihar Jigawa

January 28, 2023
Masani: Sin Za Ta Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Duniya A Shekarar 2023

Masani: Sin Za Ta Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Duniya A Shekarar 2023

January 28, 2023
Matsalolin Da APC Ta Jefa ‘Yan Nijeriya Ya Kamata Su Zama Darasi -Jarman Makarfi

Matsalolin Da APC Ta Jefa ‘Yan Nijeriya Ya Kamata Su Zama Darasi -Jarman Makarfi

January 28, 2023
Dole A Hada Karfi Wajen Dakile Bazuwar Makamai A Afirka –Buhari

Ba Don A Wahalar Da Talaka AKa Sauya Kudin Nijeriya Ba —Buhari 

January 28, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.