ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karancin Man Fetur Da Sauya Kudade Shiri Ne Na Hana Zaben 2023 —Tinubu

by Sadiq
3 years ago
Tinubu

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, ya ayyana matsalar karancin man fetur da kuma shirin sauya fasalin kudi da Babban Bankin Nijeriya (CBN), ya bullo da shi a matsayin wani shiri na kawo tsaiko ga zabe mai zuwa.

Tinubu ya bukaci ‘yan Nijeriya da kada su bari karancin man fetur ya sanyaya musu guiwa kan gudanar da ayyukansu na yau da kullum.

  • Ministan Harkokin Wajen Argentina: Sin Muhimmiyar Abokiyar Cinikayya Ce Ta Argentina
  • Xi Jinping Ya Gabatar Da Sakon Bidiyo Ga Taron Koli Karo Na 7 Na Kungiyar Kasashen Latin Amurka Da Caribbean

Tinubu ya bayyana karara cewa karancin man fetur da ake fama da shi tamkar zagon kasa ne sannan ya danganta lamarin da cewar da gangan na haddasa shi.

ADVERTISEMENT

Dan takarar na APC ya bayyana haka ne a Abeokuta, yayin yakin neman zabensa a Jihar Ogun.

Yayin zargin cewar an hada baki da yin barna wajen samar da wutar lantarki, inda ya danganta sauya fasalin kudade da aka yi a matsayin wani shiri na dagula wa mutane lissafi.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

“Ko sun ce babu mai a kasa, za mu yi tattaki don kada kuri’a. Sum yi barna da yawa don haka za su iya cewa, babu mai. Wannan zai iya haifar da rikici ta hanyar zagon kasa ga wadatar mai a kasa.

“Suna yin zagon kasa ga samar da mai. Ko man fetur ko babu za mu je mu kada kuri’a kuma za mu yi nasara. Wannan juyin juya hali ne mafi girma kuma idan na fada muku, kun san abin da nake nufi. Kun san ni ne zan sauya komai.

“Sun yi ta shirin haifar da matsalar mai, amma a manta da komai. Ni, Asiwaju zan magance matsalar samar da mai har abada.

“Ni dan gida ne, na zo nan, kuma ba zan ba ku kunya ba, za mu karbi mulki.

“Wannan juyin juya hali ne, wannan zabe juyin juya hali ne. Sun yin makirci, amma za su sha kasa. Sun ce farashin mai zai karu kuma zai kai Naira 200 kowace lita.Ba sa son a gudanar da wannan zabe, suna son a murde shi,” in ji Tinubu.

Da yake magana game da tsare-tsarensa ga matasan Nijeriya, Tinubu ya yi alkawarin bullo da shirin ba da lamuni ga dalibai, tare da samar da tsarin ilimi wanda zai magance matsalolin malamai da tabbatar da cewa dalibai sun kammala karatu a lokacin da ya dace.

“Ina ba ku tabbacin abu daya: zan bai wa dalibai lamuni. Babu wanda zai daina zuwa Jami’ar saboda kudin makaranta. Ina ba ku tabbacin cewa babu wanda zai sake maimaita shekaru ba tare da ya kammala karatunsa ba.”

MASU ALAKA

Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

June 11, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano

May 5, 2026
Next Post
Qin Gang Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Ma’aikatar Harkokin Wajen Gabon Bisa Rasuwar Ministan Harkokin Wajen Kasar Michael Moussa-Adamo

Qin Gang Ya Aike Da Sakon Ta'aziyya Ga Ma'aikatar Harkokin Wajen Gabon Bisa Rasuwar Ministan Harkokin Wajen Kasar Michael Moussa-Adamo

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.