• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karancin Man Fetur Ya Haddasa Tsadar Kayan Masarufi A Zamfara

by Sadiq
3 years ago
Man Fetur

Karancin man fetur ya addabi Jihar Zamfara, wanda hakan ya haifar da tsadar rayuwa a Jihar yayin da ‘yan kasuwa ke korafin karancin man fetir da tsadar kayayyaki. 

Leadership ta rawaito cewa yawancin mazauna jihar a yanzu suna tafiya mai nisa a kafa saboda ba za su iya biyan kudin ababen hawa ba.

  • Dabara Ta Rage Ga Mai Shiga Rijiya
  • Wike: “Yakin Neman Zabe Ne Yanzu A Gaban Mu” – Rundunar Yakin Neman Zaben Atiku

Mallam Yunusa wanda ya zanta da manema labarai, ya ce isa birnin Gusau ne daga garin Danba mai tazarar kilomita bakwai da kafa.

“Na gargadi dukkan ‘yan uwana da kada su sake fitowa a 2023 da sunan zaben kowa saboda ban ga wata ribar dimokuradiyya a Nijeriya ba, musamman a Jihar Zamfara,” in ji shi.

Yunusa ya koka da cewa shi dan fansho ne yana karbar Naira 7,500 kacal a kowane wata daga gwamnatin jihar bayan ya yi wa gwamnatin jihar hidima tsawon shekaru 35 ba tare da wata kyautatawa ba.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

“Yaya Nijeriya za ta gyaru yayin da masu hannu da shuni ke kara arziki yayin da talakawa ke kara talaucewa? Dimokuradiyya kenan? Kamar yadda ya tambaya.

Da aka tambaye shi game da sake fasalin kudin, sai ya ce, al’amuran masu wawure dukiyar Nijeriya ne, talakawa ba su damu da wannan batu ba saboda shugabannin sun san kansu.

A halin da ake ciki, a ziyarar da wakilinmu ya kai wasu manyan kasuwanni a Gusau, babban birnin jihar, ya gano cewa harkokin kasuwanci na tafiyar hawainiya ba tare da hada-hadar masu saye ba.

Galibin mazauna jihar sun kuma yi korafin cewa duk da karancin man fetur da ke ci gaba da addabar kasar, amma ga dukkan alamu Jihar Zamfara ce ta fi fama da matsalar kasancewar lamarin ya gurgunta duk wasu harkokin tattalin arzikin Jihar.

“Ta yaya gwamnatin jiha za ta yi ikirarin cewa tana gamsar da kowa yayin da jama’a a jihar ke mutuwa saboda yunwa,” kamar yadda ya koka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Triumph
Manyan Labarai

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
Manyan Labarai

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Tsara Matakai 20 Na Inganta Ayyukan Kandagarki Da Shawo Kan Annobar Covid-19

Kasar Sin Ta Tsara Matakai 20 Na Inganta Ayyukan Kandagarki Da Shawo Kan Annobar Covid-19

LABARAI MASU NASABA

Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.