• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karancin Man Fetur Ya Haddasa Tsadar Kayan Masarufi A Zamfara

by Sadiq
3 years ago
Man Fetur

Karancin man fetur ya addabi Jihar Zamfara, wanda hakan ya haifar da tsadar rayuwa a Jihar yayin da ‘yan kasuwa ke korafin karancin man fetir da tsadar kayayyaki. 

Leadership ta rawaito cewa yawancin mazauna jihar a yanzu suna tafiya mai nisa a kafa saboda ba za su iya biyan kudin ababen hawa ba.

  • Dabara Ta Rage Ga Mai Shiga Rijiya
  • Wike: “Yakin Neman Zabe Ne Yanzu A Gaban Mu” – Rundunar Yakin Neman Zaben Atiku

Mallam Yunusa wanda ya zanta da manema labarai, ya ce isa birnin Gusau ne daga garin Danba mai tazarar kilomita bakwai da kafa.

“Na gargadi dukkan ‘yan uwana da kada su sake fitowa a 2023 da sunan zaben kowa saboda ban ga wata ribar dimokuradiyya a Nijeriya ba, musamman a Jihar Zamfara,” in ji shi.

Yunusa ya koka da cewa shi dan fansho ne yana karbar Naira 7,500 kacal a kowane wata daga gwamnatin jihar bayan ya yi wa gwamnatin jihar hidima tsawon shekaru 35 ba tare da wata kyautatawa ba.

LABARAI MASU NASABA

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

“Yaya Nijeriya za ta gyaru yayin da masu hannu da shuni ke kara arziki yayin da talakawa ke kara talaucewa? Dimokuradiyya kenan? Kamar yadda ya tambaya.

Da aka tambaye shi game da sake fasalin kudin, sai ya ce, al’amuran masu wawure dukiyar Nijeriya ne, talakawa ba su damu da wannan batu ba saboda shugabannin sun san kansu.

A halin da ake ciki, a ziyarar da wakilinmu ya kai wasu manyan kasuwanni a Gusau, babban birnin jihar, ya gano cewa harkokin kasuwanci na tafiyar hawainiya ba tare da hada-hadar masu saye ba.

Galibin mazauna jihar sun kuma yi korafin cewa duk da karancin man fetur da ke ci gaba da addabar kasar, amma ga dukkan alamu Jihar Zamfara ce ta fi fama da matsalar kasancewar lamarin ya gurgunta duk wasu harkokin tattalin arzikin Jihar.

“Ta yaya gwamnatin jiha za ta yi ikirarin cewa tana gamsar da kowa yayin da jama’a a jihar ke mutuwa saboda yunwa,” kamar yadda ya koka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru
Wasanni

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL
Manyan Labarai

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Tsara Matakai 20 Na Inganta Ayyukan Kandagarki Da Shawo Kan Annobar Covid-19

Kasar Sin Ta Tsara Matakai 20 Na Inganta Ayyukan Kandagarki Da Shawo Kan Annobar Covid-19

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwamnatin Kaduna Tare Da  AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.