• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karancin Takardar Kudi: Masu POS Da Bankuna Na Wasa Da Hankulan Jama’a

by Khalid Idris Doya
10 months ago
in Labarai
0
Karancin Takardar Kudi: Masu POS Da Bankuna Na Wasa Da Hankulan Jama’a
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da bukukuwan Kirsimeti da na sabuwar shekara suke kan dosowa, al’umman Nijeriya suna kan fuskantar karancin takardar kudi domin hada-hadar yau da gobe. Wasu mazauna Abuja da wasu jihohi da aka yi hira da su, sun koka kan wahalar samun takardar kudi da suke sha a fadin kasar nan.

Wannan kuwa na zuwa ne daidai lokacin da Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya ce sama da naira tiriliyan 3.87 aka fitar da su daga bankuna domin amfanin jama’a.

  • CBN Ya Bayyana Shirin Kakaba Wa Bankuna Takunkumi
  • Gwamnan Sakkwato Ya Gabatar Da Kasafin Kudin 2025 Na Biliyan 526

Bayanan na cewa kawo 93.34 na takardar kudin na hannun daidaikun mutane da ‘yan kasuwa, inda kuma sauran kaso 6.66 kacal ke yawo a tsakanin bankuna, inda jama’a kuma ke ci gaba da dogara da amfani da takardar kudin duk da inganta tsare-tsaren hada-hadar kudade ta yanar gizo.

An tattaro cewa ‘yan kasuwa musamman da suke karkara sun fi shan wahalar karancin takardar kudi, yayin da masu sayar da kayayyaki suka fi bukatar takardar kudi fiye da ta yanar gizo, kamar manoma a yankunan karkara, inda suke kin amincewa da hada-hadar yanar gizo kan danfara da suka yi ta fuskanta a baya.

Sakataren kungiyar masu POS a Nijeriya (APOSUN), Mista Isah Zakari, ya ce abubuwa da dama ne suka janyo karancin takardar kudi.

Labarai Masu Nasaba

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

Yayin da yake daura alhalin hakan ga bankuna, inda ya ce tun daga watan Disamban 2023, bankuna suka rage ba su takardar kudi yadda suke bukata, sai dai suna zaban wasu su ba su da yawa.

Ya yi zargin cewa wuraren POS da dama mallakin wasu ma’aikatan banki ne, ya kara da cewa suna fitar da kudaden da za su rabar da kwastomominsu a wajen POS dinsu, yayin da saura kuma ke fama da rashin kudin.

Wasu bankuna a cikin Abuja suna da iyakan adadin kudin da suke iya bai wa mutane, hatta na ATM ma mutum ba zai iya cire kudi da yawa ba.

Masu POS din sun ce bankuna sun tilasta musu yanzu ba su da wasu mafita illa suke neman takardar kudi daga wajen ‘yan kasuwa ko gidajen mai, inda suka ce hakan ya sanya suka kara yawan kudin da suke cazan mutane.

Wani mai sana’ar hannu, Mista John Otafu, ya ce suna fuskantar wahala sosai wajen mu’amala da takardar kudi sakamakon karancinsa da rashin samunsa, yayin da ba su samun ko sisi a na’urorin ATM.

Wata mai sana’ar saida abinci, Titilayo Abayomi, ta ce, yanzu ta dauki dabarar boye takardar kudinta da kanta domin in ta ajiye a banki ba ta samunsu a lokacin da take so.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: POS
ShareTweetSendShare
Previous Post

INEC Ta Caccaki Gwamnonin PDP Kan Zargin Tafka Magudi A Zaben Edo

Next Post

Yara 160,000 Ke Rayuwa Da Cutar Ƙanjamau A Nijeriya —NACA

Related

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 
Labarai

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

2 minutes ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

3 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

5 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

18 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

19 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

21 hours ago
Next Post
Yara 160,000 Ke Rayuwa Da Cutar Ƙanjamau A Nijeriya —NACA

Yara 160,000 Ke Rayuwa Da Cutar Ƙanjamau A Nijeriya —NACA

LABARAI MASU NASABA

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.