• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karancin Takardar Kudi: Masu POS Da Bankuna Na Wasa Da Hankulan Jama’a

by Khalid Idris Doya
7 months ago
in Labarai
0
Karancin Takardar Kudi: Masu POS Da Bankuna Na Wasa Da Hankulan Jama’a
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da bukukuwan Kirsimeti da na sabuwar shekara suke kan dosowa, al’umman Nijeriya suna kan fuskantar karancin takardar kudi domin hada-hadar yau da gobe. Wasu mazauna Abuja da wasu jihohi da aka yi hira da su, sun koka kan wahalar samun takardar kudi da suke sha a fadin kasar nan.

Wannan kuwa na zuwa ne daidai lokacin da Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya ce sama da naira tiriliyan 3.87 aka fitar da su daga bankuna domin amfanin jama’a.

  • CBN Ya Bayyana Shirin Kakaba Wa Bankuna Takunkumi
  • Gwamnan Sakkwato Ya Gabatar Da Kasafin Kudin 2025 Na Biliyan 526

Bayanan na cewa kawo 93.34 na takardar kudin na hannun daidaikun mutane da ‘yan kasuwa, inda kuma sauran kaso 6.66 kacal ke yawo a tsakanin bankuna, inda jama’a kuma ke ci gaba da dogara da amfani da takardar kudin duk da inganta tsare-tsaren hada-hadar kudade ta yanar gizo.

An tattaro cewa ‘yan kasuwa musamman da suke karkara sun fi shan wahalar karancin takardar kudi, yayin da masu sayar da kayayyaki suka fi bukatar takardar kudi fiye da ta yanar gizo, kamar manoma a yankunan karkara, inda suke kin amincewa da hada-hadar yanar gizo kan danfara da suka yi ta fuskanta a baya.

Sakataren kungiyar masu POS a Nijeriya (APOSUN), Mista Isah Zakari, ya ce abubuwa da dama ne suka janyo karancin takardar kudi.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

Yayin da yake daura alhalin hakan ga bankuna, inda ya ce tun daga watan Disamban 2023, bankuna suka rage ba su takardar kudi yadda suke bukata, sai dai suna zaban wasu su ba su da yawa.

Ya yi zargin cewa wuraren POS da dama mallakin wasu ma’aikatan banki ne, ya kara da cewa suna fitar da kudaden da za su rabar da kwastomominsu a wajen POS dinsu, yayin da saura kuma ke fama da rashin kudin.

Wasu bankuna a cikin Abuja suna da iyakan adadin kudin da suke iya bai wa mutane, hatta na ATM ma mutum ba zai iya cire kudi da yawa ba.

Masu POS din sun ce bankuna sun tilasta musu yanzu ba su da wasu mafita illa suke neman takardar kudi daga wajen ‘yan kasuwa ko gidajen mai, inda suka ce hakan ya sanya suka kara yawan kudin da suke cazan mutane.

Wani mai sana’ar hannu, Mista John Otafu, ya ce suna fuskantar wahala sosai wajen mu’amala da takardar kudi sakamakon karancinsa da rashin samunsa, yayin da ba su samun ko sisi a na’urorin ATM.

Wata mai sana’ar saida abinci, Titilayo Abayomi, ta ce, yanzu ta dauki dabarar boye takardar kudinta da kanta domin in ta ajiye a banki ba ta samunsu a lokacin da take so.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: POS
ShareTweetSendShare
Previous Post

INEC Ta Caccaki Gwamnonin PDP Kan Zargin Tafka Magudi A Zaben Edo

Next Post

Yara 160,000 Ke Rayuwa Da Cutar Ƙanjamau A Nijeriya —NACA

Related

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

14 minutes ago
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210
Manyan Labarai

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

1 hour ago
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

3 hours ago
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji
Manyan Labarai

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

5 hours ago
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

6 hours ago
Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

8 hours ago
Next Post
Yara 160,000 Ke Rayuwa Da Cutar Ƙanjamau A Nijeriya —NACA

Yara 160,000 Ke Rayuwa Da Cutar Ƙanjamau A Nijeriya —NACA

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

June 26, 2025
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

June 26, 2025
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

June 26, 2025
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

June 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.