• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karancin Takardar Kudi: Masu POS Da Bankuna Na Wasa Da Hankulan Jama’a

by Khalid Idris Doya
6 months ago
in Labarai
0
Karancin Takardar Kudi: Masu POS Da Bankuna Na Wasa Da Hankulan Jama’a
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da bukukuwan Kirsimeti da na sabuwar shekara suke kan dosowa, al’umman Nijeriya suna kan fuskantar karancin takardar kudi domin hada-hadar yau da gobe. Wasu mazauna Abuja da wasu jihohi da aka yi hira da su, sun koka kan wahalar samun takardar kudi da suke sha a fadin kasar nan.

Wannan kuwa na zuwa ne daidai lokacin da Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya ce sama da naira tiriliyan 3.87 aka fitar da su daga bankuna domin amfanin jama’a.

  • CBN Ya Bayyana Shirin Kakaba Wa Bankuna Takunkumi
  • Gwamnan Sakkwato Ya Gabatar Da Kasafin Kudin 2025 Na Biliyan 526

Bayanan na cewa kawo 93.34 na takardar kudin na hannun daidaikun mutane da ‘yan kasuwa, inda kuma sauran kaso 6.66 kacal ke yawo a tsakanin bankuna, inda jama’a kuma ke ci gaba da dogara da amfani da takardar kudin duk da inganta tsare-tsaren hada-hadar kudade ta yanar gizo.

An tattaro cewa ‘yan kasuwa musamman da suke karkara sun fi shan wahalar karancin takardar kudi, yayin da masu sayar da kayayyaki suka fi bukatar takardar kudi fiye da ta yanar gizo, kamar manoma a yankunan karkara, inda suke kin amincewa da hada-hadar yanar gizo kan danfara da suka yi ta fuskanta a baya.

Sakataren kungiyar masu POS a Nijeriya (APOSUN), Mista Isah Zakari, ya ce abubuwa da dama ne suka janyo karancin takardar kudi.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Yayin da yake daura alhalin hakan ga bankuna, inda ya ce tun daga watan Disamban 2023, bankuna suka rage ba su takardar kudi yadda suke bukata, sai dai suna zaban wasu su ba su da yawa.

Ya yi zargin cewa wuraren POS da dama mallakin wasu ma’aikatan banki ne, ya kara da cewa suna fitar da kudaden da za su rabar da kwastomominsu a wajen POS dinsu, yayin da saura kuma ke fama da rashin kudin.

Wasu bankuna a cikin Abuja suna da iyakan adadin kudin da suke iya bai wa mutane, hatta na ATM ma mutum ba zai iya cire kudi da yawa ba.

Masu POS din sun ce bankuna sun tilasta musu yanzu ba su da wasu mafita illa suke neman takardar kudi daga wajen ‘yan kasuwa ko gidajen mai, inda suka ce hakan ya sanya suka kara yawan kudin da suke cazan mutane.

Wani mai sana’ar hannu, Mista John Otafu, ya ce suna fuskantar wahala sosai wajen mu’amala da takardar kudi sakamakon karancinsa da rashin samunsa, yayin da ba su samun ko sisi a na’urorin ATM.

Wata mai sana’ar saida abinci, Titilayo Abayomi, ta ce, yanzu ta dauki dabarar boye takardar kudinta da kanta domin in ta ajiye a banki ba ta samunsu a lokacin da take so.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: POS
ShareTweetSendShare
Previous Post

INEC Ta Caccaki Gwamnonin PDP Kan Zargin Tafka Magudi A Zaben Edo

Next Post

Yara 160,000 Ke Rayuwa Da Cutar Ƙanjamau A Nijeriya —NACA

Related

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

51 minutes ago
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa
Labarai

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

2 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

3 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

4 hours ago
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 
Labarai

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

12 hours ago
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe
Labarai

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

13 hours ago
Next Post
Yara 160,000 Ke Rayuwa Da Cutar Ƙanjamau A Nijeriya —NACA

Yara 160,000 Ke Rayuwa Da Cutar Ƙanjamau A Nijeriya —NACA

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.