• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karancin Takardar Kudi: Masu POS Da Bankuna Na Wasa Da Hankulan Jama’a

by Khalid Idris Doya
11 months ago
Pos

Yayin da bukukuwan Kirsimeti da na sabuwar shekara suke kan dosowa, al’umman Nijeriya suna kan fuskantar karancin takardar kudi domin hada-hadar yau da gobe. Wasu mazauna Abuja da wasu jihohi da aka yi hira da su, sun koka kan wahalar samun takardar kudi da suke sha a fadin kasar nan.

Wannan kuwa na zuwa ne daidai lokacin da Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya ce sama da naira tiriliyan 3.87 aka fitar da su daga bankuna domin amfanin jama’a.

  • CBN Ya Bayyana Shirin Kakaba Wa Bankuna Takunkumi
  • Gwamnan Sakkwato Ya Gabatar Da Kasafin Kudin 2025 Na Biliyan 526

Bayanan na cewa kawo 93.34 na takardar kudin na hannun daidaikun mutane da ‘yan kasuwa, inda kuma sauran kaso 6.66 kacal ke yawo a tsakanin bankuna, inda jama’a kuma ke ci gaba da dogara da amfani da takardar kudin duk da inganta tsare-tsaren hada-hadar kudade ta yanar gizo.

An tattaro cewa ‘yan kasuwa musamman da suke karkara sun fi shan wahalar karancin takardar kudi, yayin da masu sayar da kayayyaki suka fi bukatar takardar kudi fiye da ta yanar gizo, kamar manoma a yankunan karkara, inda suke kin amincewa da hada-hadar yanar gizo kan danfara da suka yi ta fuskanta a baya.

Sakataren kungiyar masu POS a Nijeriya (APOSUN), Mista Isah Zakari, ya ce abubuwa da dama ne suka janyo karancin takardar kudi.

LABARAI MASU NASABA

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Yayin da yake daura alhalin hakan ga bankuna, inda ya ce tun daga watan Disamban 2023, bankuna suka rage ba su takardar kudi yadda suke bukata, sai dai suna zaban wasu su ba su da yawa.

Ya yi zargin cewa wuraren POS da dama mallakin wasu ma’aikatan banki ne, ya kara da cewa suna fitar da kudaden da za su rabar da kwastomominsu a wajen POS dinsu, yayin da saura kuma ke fama da rashin kudin.

Wasu bankuna a cikin Abuja suna da iyakan adadin kudin da suke iya bai wa mutane, hatta na ATM ma mutum ba zai iya cire kudi da yawa ba.

Masu POS din sun ce bankuna sun tilasta musu yanzu ba su da wasu mafita illa suke neman takardar kudi daga wajen ‘yan kasuwa ko gidajen mai, inda suka ce hakan ya sanya suka kara yawan kudin da suke cazan mutane.

Wani mai sana’ar hannu, Mista John Otafu, ya ce suna fuskantar wahala sosai wajen mu’amala da takardar kudi sakamakon karancinsa da rashin samunsa, yayin da ba su samun ko sisi a na’urorin ATM.

Wata mai sana’ar saida abinci, Titilayo Abayomi, ta ce, yanzu ta dauki dabarar boye takardar kudinta da kanta domin in ta ajiye a banki ba ta samunsu a lokacin da take so.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal
Labarai

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260
Manyan Labarai

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
Next Post
Yara 160,000 Ke Rayuwa Da Cutar Ƙanjamau A Nijeriya —NACA

Yara 160,000 Ke Rayuwa Da Cutar Ƙanjamau A Nijeriya —NACA

LABARAI MASU NASABA

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025
Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

October 28, 2025
Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

October 28, 2025
gaza

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.