ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Hukumomi

Kusan shekara guda bayan hakaN hukuncin Kotun koli da ta zantar kan bai wa kananan hukumomin Nijeria 774 ‘yan cin gashin kai, amma har yanzu ba a aiwatar da shi ba.

Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi ya bayyana cewa duk jihar da ta ki aiwatar da hukuncin za ta a fuskanci mummunar sakamako.

  • Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu
  • Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

A cewar ministan shari’a, alhakin aiwatar da hukuncin da tabbatar da bai wa kananan hukumomi kudadensu tsari kai tsaye yana karkashin ikon ofishin babban mai kula da kudi na gwamnatin tarayya.

ADVERTISEMENT

Ba a bayyana cewa ko ministan shari’a ya rubuta wa ofishin mai kula da kudi na gwamnatin tarayya wasika kan umarnin aiwatar da hukuncin kotun kolin ba.

Mai magana da yawun ministan sharia, Kamarudeen Ogundele, ya shaida wa manema labarai cewa batun aiwatar da hukuncin ya wuce yadda ake tsammani.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Ya ce a nemi bayani daga wurare daban-daban kamar Kungiyar Ma’aikatan Kananan Hukumomin Nijeriya (NULGE) da Ma’aikatar Kudi, ya kara da cewa sakataren gwamnatin tarayya shi ne shugaban kwamitin aiwatar da hukuncin.

Abubuwan da mutane yawa suke gnin ya janyo jinkirta aiwatar da hukuncin shi ne, shigar da sabon sharadi daga Babban Bankin Nijeriya (CBN), wanda ke bukatar dukkanin hukumomin gwamnati 774 su bayar da akalla shekaru biyu na rahotannin kudinsu kafin su iya karbar kasafin kudadensu kai tsaye daga asusun gwamnatin tarayya.

Babban bankin ya bayyana cewa dole ne gwamnatocin kananan hukumomi su cika bukatun kafin su bude asusu don kura musu kudadensu kai tsaye.

Ka’idojin da aka gindaya wa kananan hukumomin ya kara janyo tsaiko wajen jinkirta aiwatar da ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomi.

Ko da yake, yunkurin farko na jinkirta aiwatar da hukuncin shi ne, tsawon watanni uku da gwamnatin tarayya ta bai gwamnonin na gudanar da shirye-shirye a watan Agusta na 2024.

Gwamnatin tarayya da gwamnonin jihohi sun yarda da dakatar da aiwatar da hukuncin har da an tantance hanyoyin biyan albashi, tabbatar da ingancin aiki, da gudanar da zaben hukumomin kananan hukumomi da sauran batutuwa.

Kungiyar Shugabannin Kananan Hukumomin Nijeriya (ALGON), ta hannun sakatarenta, Muhammed Abubakar, ta yi korafin cewa rashin aiwatar da hukuncin ta ta’allaka ne bisa umarnin da ministan shari’a na tilasta wa CBN wajen bude asusu dukkan kananan hukumomi.

ALGON ta ce rashin bayar da umurnin ya kawo cikas ga fara zantar da hukuncin kotun.

A cikin wannan lamari, ana zargin wasu gwamnoni da yin amfani da ikonsu wajen musgunawa da kuma matsin lamba ga shugabannin kananan hukumomi don kar su bude asusun da za tura musu kasun kai tsaye.

Ana ce wasu gwamnan suna matukar adawa da bude asusun a CBN, kasancewar hakan zai hana su samun damar yin amfani da kudaden kananan hukumomi da suka dade suna juyawa.

Saboda haka, ana zargin sun bai wa shugabannin kananan hukumomi umurnin kar su yarda su bude asusun a Babban Banki Nijeriya.

Idan za a iya tunawa dai, ministan shari’a ya shigar da karar a kotun koli a madadin gwamnatin tarayya da kananan hukumomi 774, yana rokon kotun ta ba da cikakken ‘yanci da bayar da kudade kai tsaye ga kananan hukumomi daga asusun tarayya.

Kotun ta duba karar sannan ta amince da wannan bukata tare da bayar da umarnin cewa a dunga bai wa kananan hukumomin kasunsu kai tsaye ba tare da gwamnonin jihohi sun rike kudaden ba wanda ya saba wa tsarin dimokuradiyya.

Shari’ar mai al’kalai bakwai, wanda ke karkashin jgorancin, Mai Shari’a Emmanuel Agim, ya bayyana cewa Nijeriya na da bangarori guda uku na gwamnati, wadanda suka hada da gwamnatin tarayya, gwamnatin jiha, da gwamnatin karamar hukumu, kuma babu wata gwamnatin jiha da ke da ikon nada kwamitin riko na kananan hukumomi saboda gwamnatin karamar hukuma ana zaben ta ne karkashin tsarin dimokuradiyya.

Kotun ta ce amfani da kwamitin riko ya saba wa kundin tsarin mulki na shekarar 1999, kuma ta kara da cewa gwamnatocin jihohi suna ci gaba da jawo mummunan rudani ta hanyar kin yarda a gudanar da zaben kananan hukumomi ta hanyar dimokuradiyya a jihohisu said ai su nada kwamitin riko ko kuma su dora wadanda suka so.

Kotun koli ta umarci a gaggauta fara aiwatar da hukuncin nan take.

Bayan wata guda da yanke hukuncin, gwamnatin tarayya ta kafa kwamitin don aiwatar da hukuncin, wanda ke karkashin shugabancin sakataren gwamnatin tarayya, Sanata George Akume. Kwamitin ya kashe tsawon yana tattaunawa kuma har ya mika rahotonsa.

Duk da haka, abun mamakin shi ne, bayan wata daya da zartar da hukuncin kotun kolin wacce ta bayar da umurnin a gaggauta aiwatar da shi, amma har yanzu an kasa aiwatar da hukuncin.

Hukumomi
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.