ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Hukumomi

Kusan shekara guda bayan hakaN hukuncin Kotun koli da ta zantar kan bai wa kananan hukumomin Nijeria 774 ‘yan cin gashin kai, amma har yanzu ba a aiwatar da shi ba.

Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi ya bayyana cewa duk jihar da ta ki aiwatar da hukuncin za ta a fuskanci mummunar sakamako.

  • Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu
  • Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

A cewar ministan shari’a, alhakin aiwatar da hukuncin da tabbatar da bai wa kananan hukumomi kudadensu tsari kai tsaye yana karkashin ikon ofishin babban mai kula da kudi na gwamnatin tarayya.

ADVERTISEMENT

Ba a bayyana cewa ko ministan shari’a ya rubuta wa ofishin mai kula da kudi na gwamnatin tarayya wasika kan umarnin aiwatar da hukuncin kotun kolin ba.

Mai magana da yawun ministan sharia, Kamarudeen Ogundele, ya shaida wa manema labarai cewa batun aiwatar da hukuncin ya wuce yadda ake tsammani.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Ya ce a nemi bayani daga wurare daban-daban kamar Kungiyar Ma’aikatan Kananan Hukumomin Nijeriya (NULGE) da Ma’aikatar Kudi, ya kara da cewa sakataren gwamnatin tarayya shi ne shugaban kwamitin aiwatar da hukuncin.

Abubuwan da mutane yawa suke gnin ya janyo jinkirta aiwatar da hukuncin shi ne, shigar da sabon sharadi daga Babban Bankin Nijeriya (CBN), wanda ke bukatar dukkanin hukumomin gwamnati 774 su bayar da akalla shekaru biyu na rahotannin kudinsu kafin su iya karbar kasafin kudadensu kai tsaye daga asusun gwamnatin tarayya.

Babban bankin ya bayyana cewa dole ne gwamnatocin kananan hukumomi su cika bukatun kafin su bude asusu don kura musu kudadensu kai tsaye.

Ka’idojin da aka gindaya wa kananan hukumomin ya kara janyo tsaiko wajen jinkirta aiwatar da ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomi.

Ko da yake, yunkurin farko na jinkirta aiwatar da hukuncin shi ne, tsawon watanni uku da gwamnatin tarayya ta bai gwamnonin na gudanar da shirye-shirye a watan Agusta na 2024.

Gwamnatin tarayya da gwamnonin jihohi sun yarda da dakatar da aiwatar da hukuncin har da an tantance hanyoyin biyan albashi, tabbatar da ingancin aiki, da gudanar da zaben hukumomin kananan hukumomi da sauran batutuwa.

Kungiyar Shugabannin Kananan Hukumomin Nijeriya (ALGON), ta hannun sakatarenta, Muhammed Abubakar, ta yi korafin cewa rashin aiwatar da hukuncin ta ta’allaka ne bisa umarnin da ministan shari’a na tilasta wa CBN wajen bude asusu dukkan kananan hukumomi.

ALGON ta ce rashin bayar da umurnin ya kawo cikas ga fara zantar da hukuncin kotun.

A cikin wannan lamari, ana zargin wasu gwamnoni da yin amfani da ikonsu wajen musgunawa da kuma matsin lamba ga shugabannin kananan hukumomi don kar su bude asusun da za tura musu kasun kai tsaye.

Ana ce wasu gwamnan suna matukar adawa da bude asusun a CBN, kasancewar hakan zai hana su samun damar yin amfani da kudaden kananan hukumomi da suka dade suna juyawa.

Saboda haka, ana zargin sun bai wa shugabannin kananan hukumomi umurnin kar su yarda su bude asusun a Babban Banki Nijeriya.

Idan za a iya tunawa dai, ministan shari’a ya shigar da karar a kotun koli a madadin gwamnatin tarayya da kananan hukumomi 774, yana rokon kotun ta ba da cikakken ‘yanci da bayar da kudade kai tsaye ga kananan hukumomi daga asusun tarayya.

Kotun ta duba karar sannan ta amince da wannan bukata tare da bayar da umarnin cewa a dunga bai wa kananan hukumomin kasunsu kai tsaye ba tare da gwamnonin jihohi sun rike kudaden ba wanda ya saba wa tsarin dimokuradiyya.

Shari’ar mai al’kalai bakwai, wanda ke karkashin jgorancin, Mai Shari’a Emmanuel Agim, ya bayyana cewa Nijeriya na da bangarori guda uku na gwamnati, wadanda suka hada da gwamnatin tarayya, gwamnatin jiha, da gwamnatin karamar hukumu, kuma babu wata gwamnatin jiha da ke da ikon nada kwamitin riko na kananan hukumomi saboda gwamnatin karamar hukuma ana zaben ta ne karkashin tsarin dimokuradiyya.

Kotun ta ce amfani da kwamitin riko ya saba wa kundin tsarin mulki na shekarar 1999, kuma ta kara da cewa gwamnatocin jihohi suna ci gaba da jawo mummunan rudani ta hanyar kin yarda a gudanar da zaben kananan hukumomi ta hanyar dimokuradiyya a jihohisu said ai su nada kwamitin riko ko kuma su dora wadanda suka so.

Kotun koli ta umarci a gaggauta fara aiwatar da hukuncin nan take.

Bayan wata guda da yanke hukuncin, gwamnatin tarayya ta kafa kwamitin don aiwatar da hukuncin, wanda ke karkashin shugabancin sakataren gwamnatin tarayya, Sanata George Akume. Kwamitin ya kashe tsawon yana tattaunawa kuma har ya mika rahotonsa.

Duk da haka, abun mamakin shi ne, bayan wata daya da zartar da hukuncin kotun kolin wacce ta bayar da umurnin a gaggauta aiwatar da shi, amma har yanzu an kasa aiwatar da hukuncin.

Hukumomi
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.