• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karin Harajin Amurka Ba Zai Dakile Sashen Kere-Keren Kasar Sin Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Karin Harajin Amurka Ba Zai Dakile Sashen Kere-Keren Kasar Sin Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A baya bayan nan bangaren kasar Amurka na ci gaba da aiwatar da matakai daban daban na karin haraji kan hajojin kasar Sin dake shiga Amurka, musamman hajojin da suka shafi na manyan fasahohi, da ababen hawa masu hade da yanar gizo, da karafa da dangoginsu, matakin da masharhanta ke kallo a matsayin wata dabara da kokarin dakile ci gaban masana’antun kere-kere na Sin, duk da cewa hakan ba Sin din kadai zai illata ba, har ma da tattalin arzikin ita kanta Amurka.

 

A baya bayan nan, an ga yadda gwamnatin Amurka ta ayyana manufar kara haraji kan irin wadannan hajoji, ciki har da karin harajin kaso 100 kan ababen hawa masu aiki da lantarki ko EVs kirar kasar Sin, da karin kaso 50 bisa dari kan sassan na’urar samar da lantarki ta amfani da hasken rana ko solar, da karin kaso 25 bisa dari kan karafa da goran ruwa, da batiran EVs, da sauran wasu sanadarai masu nasaba, manufar da a cewar ofishin wakilcin cinikayya na Amurka za ta fara aiki tun daga ranar Juma’a 27 ga watan nan.

  • Sin Na Adawa Da Matsayin Amurka Na Shirin Dakatar Da Amfani Da Ababen Hawa Dake Hade Da Yanar Gizo Kirar Sin
  • Sin Ta Kira Taron Nazarin Yanayi Da Aikin Raya Tattalin Arzikin Kasar 

Har kullum ’yan siyasar Amurka na amfani da batun karin haraji, da sauran karin matakan baiwa kasuwar gida kariya, a matsayin makamin dakile kasar Sin ta fuskar takarar cinikayya. To sai dai kuma irin wadannan matakai sun ci karo da kyakkyawan tunani na cimma nasarar raya cinikayya, da bunkasa tattalin arziki tsakanin kasashen duniya.

 

Labarai Masu Nasaba

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

Tuni kasar Sin ta samar da tsari mai juriya na raya fannin kere-kere, wanda ke dogaro ga tarin basirar dake cikin kasar, da babbar kasuwar ta mai yalwa, don haka ba ta dogaro ga neman alfarmar wata kasa dake ketare wajen cimma burinta na raya kai.

 

Hakan na iya kara bayyana a fili, idan muka kalli kwarya-kwaryar rahoton da hukumar lura da ikon mallakar fasaha ta kasa da kasa ta fitar game da alkaluman kere-kere na duniya ko (GII) na shekarar 2024, wadanda suka nuna cewa, Sin na da tarin cibiyoyin kere-keren kimiyya da fasaha har 26, cikin jimillar 100 dake kan gaba a duniya, ta kuma tabbatar da matsayinta na jagora a duniya a wannan fanni a tsawon shekaru 2 a jere.

 

Ko shakka babu matakan baiwa kasuwa kariya ba za su warware ginshikan matsalo da kasar Amurka ke fuskanta ba, musamman a fannin takara tsakanin masana’antu. Kuma ta hanyar dora laifi ga kasar Sin, Amurka na kaucewa sahihan matakai da ya kamata ta dauka na bunkasa tattalin arzikinta. Don haka lokaci ya yi da Amurka za ta yi karatun ta nutsu, ta yi hangen nesa, tare da karkata akala zuwa ga sauye-sauye a cikin gida, da zakulo hanyoyin raya kai, maimakon baiwa kasuwa kariya, ko yin fito na fito da kasar Sin. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Batun Amfani Da Na’urori Masu Basira A Fannin Watsa Labarai Na Sin Na 2024

Next Post

An Kashe Jagororin ‘Yan Bindiga, Sani Black Da Kachalla Makore A Zamfara

Related

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

18 hours ago
Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara
Daga Birnin Sin

Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

20 hours ago
Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka
Daga Birnin Sin

Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

23 hours ago
Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

24 hours ago
Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

2 days ago
CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025
Daga Birnin Sin

CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025

2 days ago
Next Post
Sojoji

An Kashe Jagororin 'Yan Bindiga, Sani Black Da Kachalla Makore A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

June 2, 2025
Mataimakin shugaban kasa

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

June 2, 2025

Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

June 2, 2025
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

June 2, 2025
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

June 2, 2025
Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

June 2, 2025
Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

June 2, 2025
Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

June 2, 2025
2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu

2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu

June 2, 2025
Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.