• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karin Harajin Amurka Ba Zai Dakile Sashen Kere-Keren Kasar Sin Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Amurka

A baya bayan nan bangaren kasar Amurka na ci gaba da aiwatar da matakai daban daban na karin haraji kan hajojin kasar Sin dake shiga Amurka, musamman hajojin da suka shafi na manyan fasahohi, da ababen hawa masu hade da yanar gizo, da karafa da dangoginsu, matakin da masharhanta ke kallo a matsayin wata dabara da kokarin dakile ci gaban masana’antun kere-kere na Sin, duk da cewa hakan ba Sin din kadai zai illata ba, har ma da tattalin arzikin ita kanta Amurka.

 

A baya bayan nan, an ga yadda gwamnatin Amurka ta ayyana manufar kara haraji kan irin wadannan hajoji, ciki har da karin harajin kaso 100 kan ababen hawa masu aiki da lantarki ko EVs kirar kasar Sin, da karin kaso 50 bisa dari kan sassan na’urar samar da lantarki ta amfani da hasken rana ko solar, da karin kaso 25 bisa dari kan karafa da goran ruwa, da batiran EVs, da sauran wasu sanadarai masu nasaba, manufar da a cewar ofishin wakilcin cinikayya na Amurka za ta fara aiki tun daga ranar Juma’a 27 ga watan nan.

  • Sin Na Adawa Da Matsayin Amurka Na Shirin Dakatar Da Amfani Da Ababen Hawa Dake Hade Da Yanar Gizo Kirar Sin
  • Sin Ta Kira Taron Nazarin Yanayi Da Aikin Raya Tattalin Arzikin Kasar 

Har kullum ’yan siyasar Amurka na amfani da batun karin haraji, da sauran karin matakan baiwa kasuwar gida kariya, a matsayin makamin dakile kasar Sin ta fuskar takarar cinikayya. To sai dai kuma irin wadannan matakai sun ci karo da kyakkyawan tunani na cimma nasarar raya cinikayya, da bunkasa tattalin arziki tsakanin kasashen duniya.

 

LABARAI MASU NASABA

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

Tuni kasar Sin ta samar da tsari mai juriya na raya fannin kere-kere, wanda ke dogaro ga tarin basirar dake cikin kasar, da babbar kasuwar ta mai yalwa, don haka ba ta dogaro ga neman alfarmar wata kasa dake ketare wajen cimma burinta na raya kai.

 

Hakan na iya kara bayyana a fili, idan muka kalli kwarya-kwaryar rahoton da hukumar lura da ikon mallakar fasaha ta kasa da kasa ta fitar game da alkaluman kere-kere na duniya ko (GII) na shekarar 2024, wadanda suka nuna cewa, Sin na da tarin cibiyoyin kere-keren kimiyya da fasaha har 26, cikin jimillar 100 dake kan gaba a duniya, ta kuma tabbatar da matsayinta na jagora a duniya a wannan fanni a tsawon shekaru 2 a jere.

 

Ko shakka babu matakan baiwa kasuwa kariya ba za su warware ginshikan matsalo da kasar Amurka ke fuskanta ba, musamman a fannin takara tsakanin masana’antu. Kuma ta hanyar dora laifi ga kasar Sin, Amurka na kaucewa sahihan matakai da ya kamata ta dauka na bunkasa tattalin arzikinta. Don haka lokaci ya yi da Amurka za ta yi karatun ta nutsu, ta yi hangen nesa, tare da karkata akala zuwa ga sauye-sauye a cikin gida, da zakulo hanyoyin raya kai, maimakon baiwa kasuwa kariya, ko yin fito na fito da kasar Sin. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 
Daga Birnin Sin

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

October 22, 2025
Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11
Daga Birnin Sin

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

October 22, 2025
Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera
Daga Birnin Sin

Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

October 22, 2025
Next Post
Sojoji

An Kashe Jagororin 'Yan Bindiga, Sani Black Da Kachalla Makore A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

October 22, 2025
Majalisar NUJ Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

Majalisar NUJ Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

October 22, 2025
Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

October 22, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

October 22, 2025
Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

October 22, 2025
An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

October 22, 2025
Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

October 22, 2025
Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

October 22, 2025
Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli

Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli

October 22, 2025
Tanka

Majalisa Ta Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kai Agajin Gaggawa Ga Waɗanda Fashewar Tanka Ta Shafa A Neja

October 22, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.