Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta Jihar Kano (KAROTA), ta kama wasu matasa maza da mata guda biyar da suka tare hanya yayin da suke ɗaukar bidiyon barkwanci a babban titin da ke unguwar Hotoro, a kan gadar Muhammadu Buhari.
Mataimakin Kwamandan hukumar, Auwal Lawan Aranposu, ne ya shaida wa manema labarai cewa an kama matasan yayin da suke ɗaukar bidiyon.
- Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba
- Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?
Ya ce wannan aikin nasu na iya janyo hatsari da kuma haddasa cunkoson ababen hawa a hanya, wanda hakan barazana ce ga lafiyar al’umma.
Aranposu ya ƙara da cewa an miƙa su ga hukumar Hisbah domin ci gaba da bincike.
Hukumar KAROTA ta gargaɗi jama’a da su guji irin wannan ɗabi’a, inda ta ce ba za ta lamunci duk wani abu da zai kawo cikas ko barazana ga masu amfani da hanya ba.
Jaridar LEADERSHIP ta kuma ruwaito cewa rundunar ‘yansandan Jihar Kano ta taɓa gargaɗin masu ɗaukar bidiyo da su daina tare hanya da sunan yin fim.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp