ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karuwar Tattalin Arzikin Sin Ita Ce Damar Raya Ciniki A Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Sin

Abokaina, idan akwai dama, za ku iya zuwa birnin Lagos a kwanaki masu zuwa don halartar wasu bukukuwan baje koli masu ban sha’awa.

 

Daga ranar 5 zuwa ta 8 ga watan nan da muke ciki, za a shirya wani bikin baje kolin kayayyaki a cibiyar Landmark Centre dake tsibirin Victoria na Lagos, inda kamfanonin Sin fiye da 250 za su halarta. An ce kayayyakin da za a nuna a wajen bikin sun hada da injunan aikin gona, da na’urori masu nasaba da samar da wutar lantarki, da tufafi, da abinci, da dai sauransu. Ban da haka, daga ranar 5 zuwa ta 7 ga watan Nuwamban da muke ciki, akwai wani bikin baje koli na daban da kamfanoni 56 na lardin Zhejiang na kasar Sin za su halarta, wanda zai gudana a cibiyar TBS dake kan tsibirin Lagos.

ADVERTISEMENT
  • Zanga-zanga: Kotu Ta Bayar Da Belin Matasa 67 A Kan N670m
  • Matasa 5 Cikin Masu Zanga-zangar Tsadar Rayuwa Sun yanke Jiki Sun Faɗi A Kotu

Wadannan bukukuwa za su kai kayayyakin Sin zuwa Afirka, kana a sa’i daya, wani bikin baje kolin da zai gudana a kasar Sin, a nasa bangare zai kai dimbin kayayyakin Afirka zuwa kasuwar kasar Sin. Daga ranar 5 zuwa ta 10 ga watan Nuwamba, za a gudanar da bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su cikin kasar Sin daga ketare wato CIIE karo na 7 a birnin Shanghai na kasar Sin, inda za a nuna dimbin kayayyakin da kasar Sin take shigowa da su daga ketare, ciki har da kasashen Afirka, musamman ma bisa yarjeniyoyin da kasashen Afirka suka kulla da kasar Sin a wajen taron dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka da ya gudana a bana, misali gyadar Najeriya, da ruwan zuman kasar Rwanda, da waken gahawa na kasar Burundi, gami da kifayen kasar Madagascar, da dai sauransu.

 

LABARAI MASU NASABA

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

Wadannan bukukuwan da za su gudana sun nuna yanayi mai armashi na cudanyar Sin da Afirka a fannin tattalin arziki da na ciniki, kana wani babban dalilin da ya sa ake samun wannan yanayi mai kyau shi ne karuwar tattalin arzikin Sin, duba da cewa a watanni 9 na farko na bana, cinikin da aka yi tsakanin kasar Sin da sauran kasashe da yankuna fiye da 160 ya karu sosai, kana saurin karuwar jamillar GDP ta Sin yana kan gaba a cikin manyan tattalin arzikin duniya. Karuwar tattalin arzikin Sin, da karin matakan da gwamnatin kasar ta dauka don sa kaimi ga ci gaban tattalin arziki, sun sa kungiyoyin hada-hadar kudi irinsu Goldman Sachs, da JPMorgan Chase, da Swiss Bank, dukkansu sun daga matsayin hasashen da suka yi dangane da karuwar tattalin arzikin Sin a bana.

 

Sai dai me ya sa karuwar tattalin arzikin Sin kan janyo ci gaban bangaren ciniki da tattalin arziki a kasashen Afirka? Dalili shi ne, kasar Sin ta dukufa wajen samar da damar raya tattalin arziki ga kasashe daban daban a yayin da take kokarin zamanantar da kanta, da kuma tabbatar da ci gaba na bai daya na daukacin kasashe masu tasowa. Wadannan matakai sun dace da manufar kasar ta gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ga dukkan bil Adam. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka

November 12, 2025
CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 
Ra'ayi Riga

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

November 11, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Next Post
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.