• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karuwar Tattalin Arzikin Sin Ita Ce Damar Raya Ciniki A Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Karuwar Tattalin Arzikin Sin Ita Ce Damar Raya Ciniki A Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abokaina, idan akwai dama, za ku iya zuwa birnin Lagos a kwanaki masu zuwa don halartar wasu bukukuwan baje koli masu ban sha’awa.

 

Daga ranar 5 zuwa ta 8 ga watan nan da muke ciki, za a shirya wani bikin baje kolin kayayyaki a cibiyar Landmark Centre dake tsibirin Victoria na Lagos, inda kamfanonin Sin fiye da 250 za su halarta. An ce kayayyakin da za a nuna a wajen bikin sun hada da injunan aikin gona, da na’urori masu nasaba da samar da wutar lantarki, da tufafi, da abinci, da dai sauransu. Ban da haka, daga ranar 5 zuwa ta 7 ga watan Nuwamban da muke ciki, akwai wani bikin baje koli na daban da kamfanoni 56 na lardin Zhejiang na kasar Sin za su halarta, wanda zai gudana a cibiyar TBS dake kan tsibirin Lagos.

  • Zanga-zanga: Kotu Ta Bayar Da Belin Matasa 67 A Kan N670m
  • Matasa 5 Cikin Masu Zanga-zangar Tsadar Rayuwa Sun yanke Jiki Sun Faɗi A Kotu

Wadannan bukukuwa za su kai kayayyakin Sin zuwa Afirka, kana a sa’i daya, wani bikin baje kolin da zai gudana a kasar Sin, a nasa bangare zai kai dimbin kayayyakin Afirka zuwa kasuwar kasar Sin. Daga ranar 5 zuwa ta 10 ga watan Nuwamba, za a gudanar da bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su cikin kasar Sin daga ketare wato CIIE karo na 7 a birnin Shanghai na kasar Sin, inda za a nuna dimbin kayayyakin da kasar Sin take shigowa da su daga ketare, ciki har da kasashen Afirka, musamman ma bisa yarjeniyoyin da kasashen Afirka suka kulla da kasar Sin a wajen taron dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka da ya gudana a bana, misali gyadar Najeriya, da ruwan zuman kasar Rwanda, da waken gahawa na kasar Burundi, gami da kifayen kasar Madagascar, da dai sauransu.

 

Labarai Masu Nasaba

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

Wadannan bukukuwan da za su gudana sun nuna yanayi mai armashi na cudanyar Sin da Afirka a fannin tattalin arziki da na ciniki, kana wani babban dalilin da ya sa ake samun wannan yanayi mai kyau shi ne karuwar tattalin arzikin Sin, duba da cewa a watanni 9 na farko na bana, cinikin da aka yi tsakanin kasar Sin da sauran kasashe da yankuna fiye da 160 ya karu sosai, kana saurin karuwar jamillar GDP ta Sin yana kan gaba a cikin manyan tattalin arzikin duniya. Karuwar tattalin arzikin Sin, da karin matakan da gwamnatin kasar ta dauka don sa kaimi ga ci gaban tattalin arziki, sun sa kungiyoyin hada-hadar kudi irinsu Goldman Sachs, da JPMorgan Chase, da Swiss Bank, dukkansu sun daga matsayin hasashen da suka yi dangane da karuwar tattalin arzikin Sin a bana.

 

Sai dai me ya sa karuwar tattalin arzikin Sin kan janyo ci gaban bangaren ciniki da tattalin arziki a kasashen Afirka? Dalili shi ne, kasar Sin ta dukufa wajen samar da damar raya tattalin arziki ga kasashe daban daban a yayin da take kokarin zamanantar da kanta, da kuma tabbatar da ci gaba na bai daya na daukacin kasashe masu tasowa. Wadannan matakai sun dace da manufar kasar ta gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ga dukkan bil Adam. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zanga-zanga: Kotu Ta Bayar Da Belin Matasa 67 A Kan N670m

Next Post

Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

Related

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

2 days ago
Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Ra'ayi Riga

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

1 week ago
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

2 weeks ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

2 weeks ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

2 weeks ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

2 weeks ago
Next Post
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jama’a Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Jama’a Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.