• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karya Azumi Da Hukunce-hukuncensa

by SP. Imam Ahmad Kutubi
2 years ago
in Dausayin Musulunci
0
Karya Azumi Da Hukunce-hukuncensa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daga S.P Imam Ahmad Adam Kutubi

Idan mutum ya karya azuminsa da mantuwa, ko domin wani uzuri halattacce, zai rama azumi daya tak. Idan kuma ya karya shi ne da gangan, ko kuwa ya ki daukarsa ba da wani uzuri ba to, zai rama shi ta kowane hali, sannan kuma ya kara da yin kaffara. Watau ramuwa game da kaffara kenan. Kaffara ita ce mutum ya yi daya daga cikin wadannan abubuwa uku;

  1.  Ko dai ya ciyar da miskinai sittin ko wanne ya ba shi mudu daya na abinci… kamar dawa ko gero ko dauro ko wake ko shinkafa ko alkama. Miskini shi ne mutumin da bai mallaki abincin kwana guda a jiye ba, kome lafiyar jikinsa. Wajibi ne a samu mutum sittin ba za a ba mutum talatin ba ko wanne mudu biyu, kuma ba za a ba da dafaffen abinci ba. Mudu shi ne abin da zai cika hannuwan mutum matsakaici bayan ya hada su wuri daya, bai matse su ba kuma bai bude su da yawa ba.
  2. Ko kuwa ya ‘yanta bawa, ko baiwa lokacin da yake akwai bayi, da sharadin bawan, ko baiwar, ya zama musulmi, lafiyayye, kuma cikakken bawa.
  3. Ko kuwa ya yi azumin wata biyu cif a jere ba yankewa. Idan ya sha daya da gangan, duk na baya sun baci, sai ya soma daga farko.
    An ba mai yin kaffara zabi ya aikata duk wanda ya ga dama daga cikin ukun nan, sai dai ciyar da miskini ya fi lada, sa’an nan ‘yanta bawa ko baiwa, sannan yin azumin wata biyu..

Amai
Idan amai ya fito wa mutum bisa ga rinjaye ba da son ransa ba, har ya kawo ga bakinsa idan kam aman bai sake komawa ciki ba to azumi bai karye ba. Idan kuwa wani daga cikinsa ya sake komawa ciki ba a son ransa ba to azumi ya karye, zai rama guda daya. Idan kuwa da son ransa ne to zai yi ramuwa game da kaffara. Amma idan tun farko shi ne ya jawo yin aman nan da gangan zai rama azumi daya ko da wani abu bai koma cikinsa ba. Idan kuwa har wani abu ya sake komawa ciki da son ransa, ko da ba da son ransa ba zai yi ramuwa game da kaffara.

Jima’i
Idan mutum ya shigar da kan zakarinsa cikin farji da gangan, zai yi ramuwa game da kaffara, haka kuma ita ma macen. Amma da a ce mutum ya tarad da mace tana bacci, sai kawai ya auka mata da jima’i, duk babu azuminsu. Shi namijin zai yi ramuwa game da kaffara, macen kuma za ta rama azumi daya tak don rashin ganganci daga wajenta.

Fitar Da Maniyyi Ko Maziyyi
Idan mutum ya sumbaci mace, ko ya rungume ta ko ya yi wasa da ita ko ya yi mata mugun kallo na sha’awa, ko ya yi tunaninta a zuciyarsa, tunani mai zurfi, idan har maniyyi ya fito saboda yin daya daga cikin wadannan zai yi ramuwa game da kaffara. Idan kuwa maziyyi ne ne kawai ya fito zai rama azumi daya tak. Idan kuwa ba abin da ya fito to azumi bai baci ba, sai dai aikata dayan wadannan da rana haramun ne ga mai yawan sha’awa, makaruhi ne ga mai karancinta. Idan mutum ya yi baccin rana sai ya yi mafarki har maniyyi ya fito masa, babu komai, azuminsa bai baci ba.

Labarai Masu Nasaba

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

Azumin Mara Lafiya
Wanda ya kamu da rashin lafiya idan ciwonsa yana da sauki zai dauki azumi, idan kuma ya ga yin azumi zai kara masa rashin lafiya ko zai sa ciwon ya yi jinkirin warkewa, to an halatta masa ya ci abinci, amma ya yi ramuwa. Kuma idan zai yiwu mutum ya ajiye maganinsa har da daddare ya sha, hakan nan zai yi. Idan kuwa ba hali. Zai sha abinsa da rana amma zai yi ramuwa.

Matafiyi
An halatta wa matafiyi, tafiya irin wadda ta halatta a gajarta sallah dominta, ya sha azumi amma ya rama. Yin azumi ga matafiyi shi ya fi idan zai iya. Idan mutum ya sha azumi ga tafiyar da ba ta cika sharudda ba, sai ya yi ramuwa game da kaffara.

Shigar Kwaro Baki
Idan wani dan kwaro kamar kuda ko makamancinsa ya yi sulu ya fada cikin bakin mutum, ya kuma wuce har ciki, azumi bai baci ba.

Tsufa Ko Ciwon Kishirya Ko Yunwa
Rududdugaggen tsoho ko tsohuwa da ba sa iya yin azumi domin tsufa, da mutum mai ciwon kishirwa ko yunwa, an yafe musu yin azumi. Sai dai kowannensu an so ya yi sadaka da mudu daya ko wanne maraice, har azumi ya kare. Idan kuwa mai ciwon kishirwa yana iya yin azumi a cikin wani yanayi na shekara, kamar lokacin dari ko marka, to, ya wajaba a gare shi ya rama azumin watan Ramadana a cikin lokacin. Wato lokacin sanyi ko lokacin ruwa. In dai za su iya wadannan lokuta to wajibi ne su rama abinda suka sha.

Sauran Bayani
Ya halatta ga mai azumi ya goge bakinsa da asuwaki wanda ba ya kakkaryewa cikin baki. Idan har ya kakkarye to sai ya furje guntayen a waje. Idan kuwa ya hadiye su da mantuwa ko bisa ga rinjaye, zai rama azumi daya. Idan kuma da gangan ne ya hadiyesu zai yi ramuwa game da kaffara.
Kurar hanya ba ta bata azumi ko da ta shiga ga makogwaro, idan garin abinci ko farar kasa, ko siminti, suka shiga makogwaron mutum azumi bai baci ba amma ga mutumin da yake aikinsa yana game da wadannan abubuwa kadai. Ga waninsa kuwa azumi ya baci.

Hayakin itacen wuta ba ya karya azumi amma hayakin taba ko na turaren wuta, ko tururin tukunyar dahuwar abinci, idan ya kai ga makogwaro azumi ya karye, sai a yi ramuwa.

Idan mutum ya face majina sannan ya sake hadiyeta da gangan azuminsa ya karye, sai ya yi ramuwa, idan ba da gangan ba ne kuma azumin sa yana nan. Amma idan mutum ya tattara yawu a cikin baki, sannan ya hadiye azumi bai karye ba amma yin hakan bai kamata ba.

Idan mutum ya ga alfijir yana fitowa alhali yana cin abinci ko yana shan wani abu, sai ya daina nan da nan. Idan ya daina azumi bai baci ba. Haka kuma idan jima’i ne yake yi sai ya cire zakarinsa da sauri, azumi bai baci ba. Idan bai cire ba zai rama azumi guda daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mata 48 Da Suka Samu Tagomashin Zama ‘Yan Majalisun Wakilan Jihohi A Zaben 2023

Next Post

Fitacciyar Jarumar Nollywood Mercy Aigbe Ta Musulunta

Related

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)
Dausayin Musulunci

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

2 days ago
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)
Dausayin Musulunci

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

1 week ago
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)
Dausayin Musulunci

Darussan Hadisin Aikin Hajjin Manzon Allah S.A.W (2)

2 weeks ago
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)
Dausayin Musulunci

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

3 weeks ago
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)
Dausayin Musulunci

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)

1 month ago
Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci
Dausayin Musulunci

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

1 month ago
Next Post
Fitacciyar Jarumar Nollywood Mercy Aigbe Ta Musulunta

Fitacciyar Jarumar Nollywood Mercy Aigbe Ta Musulunta

LABARAI MASU NASABA

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.