ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasafin 2024: Tinubu Ya Umarci Ma’aikatu Su Rika Ba Da Rahoton Ayyukansu Duk Wata

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya umurci dukkan ma’aikatu da rassan gwamnati da su bayar da rahoton aikin kasafin kudi na wata-wata ga ma’aikatar kasafin kudi da tsare-tsaren tattalin arziki, wanda hakan zai tabbatar da sahihancin kwazonsu.

Umarnin ya zo ne bayan da Tinubu ya rattaba hannu a kan kudirin kasafin kudi na 2024 a ranar Litinin da ta gabata a gidan gwamnatin jim kadan bayan ya dawo Abuja daga Legas.
Da yake jawabi a wajen rattaba hannu kan kasafin kudin, shugaban kasa ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa za a bi diddigin aiwatar da kasafin kudin yadda ya kamata tare da sanya ido sosai a kai.

  • Majalisa Ta Amince Tinubu Ya Ciwo Bashin Naira Tiriliyan 7.5
  • Xi Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Iran Bisa Munanan Hare-haren Ta’addanci Da Aka Kai A Kasar

“Dukkan hanyoyin da hukumomi za su bi domin tabbatar da aiwatar da aiki tukuru kamar yadda yake a cikin kasafin kudi.

ADVERTISEMENT

“Mun umurci dukkan ma’aikatu da hukumomin gwamnati da su dunga bayar da rahoton ayyukan kasafin kudi na wata-wata ga ma’aikatar kasafin kudi da tsare-tsaren tattalin arziki, wanda hakan zai tabbatar da sahihancin gwazonsu.

“Ministan kudi zai gudanar da bita akai-akai tare da tawagar masu kula da sha’anin tattalin arziki, sannan zan jagoranci taron majalisar gudanar da tattalin arziki na lokaci-lokaci,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

Manyan abubuwan da aka fi bai wa kaso mai yawa a cikin kasafin kudin 2024 na naira tiriliyan 28.7 sun hada da tsaro, samar da ayyukan yi, inganta tattalin arzikin kasa, inganta yanayin zuba jari, bunkasa rayuwar mutane, rage talauci da kuma samar da tsaron kasa.

Shugaban kasa ya jaddada kudurinsa na inganta harkokin zuba jari da samar da al’umma mai bin doka da oda ba tare da fifita wani mutum kan doka ba, inda ya fara da wasu muhimman gyare-gyare a bangaren shari’a, wanda aka zuba wa kudaden a cikin kasafin 2024.

“Bayar da kudade ga bangaren shari’a babban kuduri ne a kokarinmu na tallafa wa al’umma wajen gudanar da adalci da bin ka’idoji. An kara kudade ga bangaren shari’a daga naira biliyan 165 zuwa naira biliyan 342,” in ji shugaban kasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas
Labarai

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
NBS
Labarai

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Next Post
NPA Ta Jagoranci Samar Da Ruwan Sha Ga Al’ummar Yankin Apapa

NPA Ta Jagoranci Samar Da Ruwan Sha Ga Al’ummar Yankin Apapa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

November 17, 2025
Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.