• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasafin 2024: Tinubu Ya Umarci Ma’aikatu Su Rika Ba Da Rahoton Ayyukansu Duk Wata

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya umurci dukkan ma’aikatu da rassan gwamnati da su bayar da rahoton aikin kasafin kudi na wata-wata ga ma’aikatar kasafin kudi da tsare-tsaren tattalin arziki, wanda hakan zai tabbatar da sahihancin kwazonsu.

Umarnin ya zo ne bayan da Tinubu ya rattaba hannu a kan kudirin kasafin kudi na 2024 a ranar Litinin da ta gabata a gidan gwamnatin jim kadan bayan ya dawo Abuja daga Legas.
Da yake jawabi a wajen rattaba hannu kan kasafin kudin, shugaban kasa ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa za a bi diddigin aiwatar da kasafin kudin yadda ya kamata tare da sanya ido sosai a kai.

  • Majalisa Ta Amince Tinubu Ya Ciwo Bashin Naira Tiriliyan 7.5
  • Xi Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Iran Bisa Munanan Hare-haren Ta’addanci Da Aka Kai A Kasar

“Dukkan hanyoyin da hukumomi za su bi domin tabbatar da aiwatar da aiki tukuru kamar yadda yake a cikin kasafin kudi.

“Mun umurci dukkan ma’aikatu da hukumomin gwamnati da su dunga bayar da rahoton ayyukan kasafin kudi na wata-wata ga ma’aikatar kasafin kudi da tsare-tsaren tattalin arziki, wanda hakan zai tabbatar da sahihancin gwazonsu.

“Ministan kudi zai gudanar da bita akai-akai tare da tawagar masu kula da sha’anin tattalin arziki, sannan zan jagoranci taron majalisar gudanar da tattalin arziki na lokaci-lokaci,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Manyan abubuwan da aka fi bai wa kaso mai yawa a cikin kasafin kudin 2024 na naira tiriliyan 28.7 sun hada da tsaro, samar da ayyukan yi, inganta tattalin arzikin kasa, inganta yanayin zuba jari, bunkasa rayuwar mutane, rage talauci da kuma samar da tsaron kasa.

Shugaban kasa ya jaddada kudurinsa na inganta harkokin zuba jari da samar da al’umma mai bin doka da oda ba tare da fifita wani mutum kan doka ba, inda ya fara da wasu muhimman gyare-gyare a bangaren shari’a, wanda aka zuba wa kudaden a cikin kasafin 2024.

“Bayar da kudade ga bangaren shari’a babban kuduri ne a kokarinmu na tallafa wa al’umma wajen gudanar da adalci da bin ka’idoji. An kara kudade ga bangaren shari’a daga naira biliyan 165 zuwa naira biliyan 342,” in ji shugaban kasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
Manyan Labarai

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya
Labarai

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Next Post
NPA Ta Jagoranci Samar Da Ruwan Sha Ga Al’ummar Yankin Apapa

NPA Ta Jagoranci Samar Da Ruwan Sha Ga Al’ummar Yankin Apapa

LABARAI MASU NASABA

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.