ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasafin 2024: Tinubu Ya Umarci Ma’aikatu Su Rika Ba Da Rahoton Ayyukansu Duk Wata

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya umurci dukkan ma’aikatu da rassan gwamnati da su bayar da rahoton aikin kasafin kudi na wata-wata ga ma’aikatar kasafin kudi da tsare-tsaren tattalin arziki, wanda hakan zai tabbatar da sahihancin kwazonsu.

Umarnin ya zo ne bayan da Tinubu ya rattaba hannu a kan kudirin kasafin kudi na 2024 a ranar Litinin da ta gabata a gidan gwamnatin jim kadan bayan ya dawo Abuja daga Legas.
Da yake jawabi a wajen rattaba hannu kan kasafin kudin, shugaban kasa ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa za a bi diddigin aiwatar da kasafin kudin yadda ya kamata tare da sanya ido sosai a kai.

  • Majalisa Ta Amince Tinubu Ya Ciwo Bashin Naira Tiriliyan 7.5
  • Xi Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Iran Bisa Munanan Hare-haren Ta’addanci Da Aka Kai A Kasar

“Dukkan hanyoyin da hukumomi za su bi domin tabbatar da aiwatar da aiki tukuru kamar yadda yake a cikin kasafin kudi.

ADVERTISEMENT

“Mun umurci dukkan ma’aikatu da hukumomin gwamnati da su dunga bayar da rahoton ayyukan kasafin kudi na wata-wata ga ma’aikatar kasafin kudi da tsare-tsaren tattalin arziki, wanda hakan zai tabbatar da sahihancin gwazonsu.

“Ministan kudi zai gudanar da bita akai-akai tare da tawagar masu kula da sha’anin tattalin arziki, sannan zan jagoranci taron majalisar gudanar da tattalin arziki na lokaci-lokaci,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Manyan abubuwan da aka fi bai wa kaso mai yawa a cikin kasafin kudin 2024 na naira tiriliyan 28.7 sun hada da tsaro, samar da ayyukan yi, inganta tattalin arzikin kasa, inganta yanayin zuba jari, bunkasa rayuwar mutane, rage talauci da kuma samar da tsaron kasa.

Shugaban kasa ya jaddada kudurinsa na inganta harkokin zuba jari da samar da al’umma mai bin doka da oda ba tare da fifita wani mutum kan doka ba, inda ya fara da wasu muhimman gyare-gyare a bangaren shari’a, wanda aka zuba wa kudaden a cikin kasafin 2024.

“Bayar da kudade ga bangaren shari’a babban kuduri ne a kokarinmu na tallafa wa al’umma wajen gudanar da adalci da bin ka’idoji. An kara kudade ga bangaren shari’a daga naira biliyan 165 zuwa naira biliyan 342,” in ji shugaban kasa.

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Next Post
NPA Ta Jagoranci Samar Da Ruwan Sha Ga Al’ummar Yankin Apapa

NPA Ta Jagoranci Samar Da Ruwan Sha Ga Al’ummar Yankin Apapa

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.