• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Da Namibia Sun Sha Alwashin Daukaka Hadin Gwiwarsu Na Cin Moriyar Juna

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
Namibia

A jiya Litinin ne zababbiyar shugabar kasar Namibia, Netumba Nandi-Ndaitwah ta gana da ministan harkokin wajen kasar Sin, kuma har ila yau mamba a kwamitin koli kan harkokin siyasa na jam’iyyar JKS, Wang Yi, a babban birnin Namibia Windhoek.

A ganawar tasu, Wang ya isar da sakon gaisuwar Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ga Shugaba Ndaitwah tare da taya ta murnar zama mace ta farko da aka zaba a matsayin shugabar kasar Namibia, kana ya yi mata fatan alheri da samun gagarumar nasara wajen gina ci gaban kasar ta Namibia.

  • Xi Da Shugaban Botswana Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alaka
  • Gwamnan Kano Ya Nemi A Rage Kuɗin Hajjin 2025

Wanga ya yi nuni da cewa, a bana an cika shekaru 35 da fara huldar diflomasiyya a tsakanin kasar Sin da Namibia, sai ya jaddada cewa hadin gwiwar dake tsakanin kasashen biyu na da matukar alfanu musamman ma a gaba.

Ya yi waiwaye adon tafiya a kan nasarar da aka samu a taron koli na dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, watau FOCAC da ya gudana a birnin Beijing a bara, lokacin da shugaban kasar Sin ya sanar da wasu tsare-tsare guda 10 na hadin gwiwa a fannin zurfafa zamanantarwa. Wang ya bayyana kudurin kasar Sin na tafiya kafada-da-kafada da Namibia domin gaggauta aiwatar da abubuwan da aka cimma a taron, don tabbatar da dorewar ci gaban da ake samu a cikakken tsararren hadin gwiwarsu.

A nata bangaren, Shugaba Ndaitwah ta bukaci Wang ya mika sakon gaisuwarta da kuma godiya ga Shugaba Xi Jinping bisa taya ta murnar lashe zaben shugaban kasar Namibia, tana mai bayyana cewa, a shekarar 2018, kasar Sin da Namibia sun daga darajar huldodinsu na diflomasiyya zuwa cikakken tsararren hadin gwiwa wanda tabbas yana da matukar alfanun gaske.

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Shugaba Ndaitwah ta kara da cewa, al’ummomin kasashen biyu sun ci gaba da sada dadadden zumuncin dake tsakaninsu kuma Namibia za ta ci gaba da gudanar da hadin gwiwar dake tsakaninsu har ma da kara daukaka shi, tare da jaddada kudurin kasar na tsayawa a kan akidar kasar Sin daya dunkulalliya.

Hakazalika, shugabar ta bayyana shirin kasar na aiwatar da sakamakon taron kolin FOCAC na Beijing da kara habaka hadin gwiwa da kasar Sin a fannonin cinikayya, da ilimi, da aikin gona, da ababen more rayuwa da kuma albarkatun makamashi domin samar wa tattalin arzikin Namibia da walwalar jama’arta sabbin damammaki da za su amfanar da al’ummomin kasashen biyu. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik
Daga Birnin Sin

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki
Daga Birnin Sin

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
Next Post
Adadin Kudin Ajiyar Sin Na Ketare Ya Ragu Zuwa Dala Tiriliyan 3.2024

Adadin Kudin Ajiyar Sin Na Ketare Ya Ragu Zuwa Dala Tiriliyan 3.2024

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.