• English
  • Business News
Monday, June 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Da Namibia Sun Sha Alwashin Daukaka Hadin Gwiwarsu Na Cin Moriyar Juna

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Da Namibia Sun Sha Alwashin Daukaka Hadin Gwiwarsu Na Cin Moriyar Juna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Litinin ne zababbiyar shugabar kasar Namibia, Netumba Nandi-Ndaitwah ta gana da ministan harkokin wajen kasar Sin, kuma har ila yau mamba a kwamitin koli kan harkokin siyasa na jam’iyyar JKS, Wang Yi, a babban birnin Namibia Windhoek.

A ganawar tasu, Wang ya isar da sakon gaisuwar Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ga Shugaba Ndaitwah tare da taya ta murnar zama mace ta farko da aka zaba a matsayin shugabar kasar Namibia, kana ya yi mata fatan alheri da samun gagarumar nasara wajen gina ci gaban kasar ta Namibia.

  • Xi Da Shugaban Botswana Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alaka
  • Gwamnan Kano Ya Nemi A Rage Kuɗin Hajjin 2025

Wanga ya yi nuni da cewa, a bana an cika shekaru 35 da fara huldar diflomasiyya a tsakanin kasar Sin da Namibia, sai ya jaddada cewa hadin gwiwar dake tsakanin kasashen biyu na da matukar alfanu musamman ma a gaba.

Ya yi waiwaye adon tafiya a kan nasarar da aka samu a taron koli na dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, watau FOCAC da ya gudana a birnin Beijing a bara, lokacin da shugaban kasar Sin ya sanar da wasu tsare-tsare guda 10 na hadin gwiwa a fannin zurfafa zamanantarwa. Wang ya bayyana kudurin kasar Sin na tafiya kafada-da-kafada da Namibia domin gaggauta aiwatar da abubuwan da aka cimma a taron, don tabbatar da dorewar ci gaban da ake samu a cikakken tsararren hadin gwiwarsu.

A nata bangaren, Shugaba Ndaitwah ta bukaci Wang ya mika sakon gaisuwarta da kuma godiya ga Shugaba Xi Jinping bisa taya ta murnar lashe zaben shugaban kasar Namibia, tana mai bayyana cewa, a shekarar 2018, kasar Sin da Namibia sun daga darajar huldodinsu na diflomasiyya zuwa cikakken tsararren hadin gwiwa wanda tabbas yana da matukar alfanun gaske.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki

Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

Shugaba Ndaitwah ta kara da cewa, al’ummomin kasashen biyu sun ci gaba da sada dadadden zumuncin dake tsakaninsu kuma Namibia za ta ci gaba da gudanar da hadin gwiwar dake tsakaninsu har ma da kara daukaka shi, tare da jaddada kudurin kasar na tsayawa a kan akidar kasar Sin daya dunkulalliya.

Hakazalika, shugabar ta bayyana shirin kasar na aiwatar da sakamakon taron kolin FOCAC na Beijing da kara habaka hadin gwiwa da kasar Sin a fannonin cinikayya, da ilimi, da aikin gona, da ababen more rayuwa da kuma albarkatun makamashi domin samar wa tattalin arzikin Namibia da walwalar jama’arta sabbin damammaki da za su amfanar da al’ummomin kasashen biyu. (Abdulrazaq Yahuza Jere)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Ki Amincewa Da Kara Kamfanoni 11 Cikin “Jerin Kamfanoni Masu Barazana Ga Amurka”

Next Post

Adadin Kudin Ajiyar Sin Na Ketare Ya Ragu Zuwa Dala Tiriliyan 3.2024

Related

Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki

1 hour ago
Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin
Daga Birnin Sin

Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

19 hours ago
Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?
Daga Birnin Sin

Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

21 hours ago
Gwamnatin Hong Kong Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru Biyar Da Kafuwar Dokar Tsaron Kasa Ta Yankin
Daga Birnin Sin

Gwamnatin Hong Kong Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru Biyar Da Kafuwar Dokar Tsaron Kasa Ta Yankin

23 hours ago
Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran

1 day ago
CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 
Daga Birnin Sin

CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 

2 days ago
Next Post
Adadin Kudin Ajiyar Sin Na Ketare Ya Ragu Zuwa Dala Tiriliyan 3.2024

Adadin Kudin Ajiyar Sin Na Ketare Ya Ragu Zuwa Dala Tiriliyan 3.2024

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki

Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki

June 23, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe

‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe

June 23, 2025
Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

June 23, 2025
Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

June 23, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Yakin Iran Da Isra’ila Ya Haifar Da Tashin Farashin Litar Man Fetur A Nijeriya

June 23, 2025
Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

June 23, 2025
Gwamnan Abba Kabir Yusuf tare da Arch. Ali Hassan

Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan

June 23, 2025
2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

June 22, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

June 22, 2025
Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

June 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.