ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Da Namibia Sun Sha Alwashin Daukaka Hadin Gwiwarsu Na Cin Moriyar Juna

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Namibia

A jiya Litinin ne zababbiyar shugabar kasar Namibia, Netumba Nandi-Ndaitwah ta gana da ministan harkokin wajen kasar Sin, kuma har ila yau mamba a kwamitin koli kan harkokin siyasa na jam’iyyar JKS, Wang Yi, a babban birnin Namibia Windhoek.

A ganawar tasu, Wang ya isar da sakon gaisuwar Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ga Shugaba Ndaitwah tare da taya ta murnar zama mace ta farko da aka zaba a matsayin shugabar kasar Namibia, kana ya yi mata fatan alheri da samun gagarumar nasara wajen gina ci gaban kasar ta Namibia.

  • Xi Da Shugaban Botswana Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alaka
  • Gwamnan Kano Ya Nemi A Rage Kuɗin Hajjin 2025

Wanga ya yi nuni da cewa, a bana an cika shekaru 35 da fara huldar diflomasiyya a tsakanin kasar Sin da Namibia, sai ya jaddada cewa hadin gwiwar dake tsakanin kasashen biyu na da matukar alfanu musamman ma a gaba.

ADVERTISEMENT

Ya yi waiwaye adon tafiya a kan nasarar da aka samu a taron koli na dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, watau FOCAC da ya gudana a birnin Beijing a bara, lokacin da shugaban kasar Sin ya sanar da wasu tsare-tsare guda 10 na hadin gwiwa a fannin zurfafa zamanantarwa. Wang ya bayyana kudurin kasar Sin na tafiya kafada-da-kafada da Namibia domin gaggauta aiwatar da abubuwan da aka cimma a taron, don tabbatar da dorewar ci gaban da ake samu a cikakken tsararren hadin gwiwarsu.

A nata bangaren, Shugaba Ndaitwah ta bukaci Wang ya mika sakon gaisuwarta da kuma godiya ga Shugaba Xi Jinping bisa taya ta murnar lashe zaben shugaban kasar Namibia, tana mai bayyana cewa, a shekarar 2018, kasar Sin da Namibia sun daga darajar huldodinsu na diflomasiyya zuwa cikakken tsararren hadin gwiwa wanda tabbas yana da matukar alfanun gaske.

LABARAI MASU NASABA

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Shugaba Ndaitwah ta kara da cewa, al’ummomin kasashen biyu sun ci gaba da sada dadadden zumuncin dake tsakaninsu kuma Namibia za ta ci gaba da gudanar da hadin gwiwar dake tsakaninsu har ma da kara daukaka shi, tare da jaddada kudurin kasar na tsayawa a kan akidar kasar Sin daya dunkulalliya.

Hakazalika, shugabar ta bayyana shirin kasar na aiwatar da sakamakon taron kolin FOCAC na Beijing da kara habaka hadin gwiwa da kasar Sin a fannonin cinikayya, da ilimi, da aikin gona, da ababen more rayuwa da kuma albarkatun makamashi domin samar wa tattalin arzikin Namibia da walwalar jama’arta sabbin damammaki da za su amfanar da al’ummomin kasashen biyu. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Namibia
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya
Namibia
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
  • Sulaiman
    Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma
  • Sulaiman
    Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin
  • Sulaiman
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

MASU ALAKA

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026
Next Post
Adadin Kudin Ajiyar Sin Na Ketare Ya Ragu Zuwa Dala Tiriliyan 3.2024

Adadin Kudin Ajiyar Sin Na Ketare Ya Ragu Zuwa Dala Tiriliyan 3.2024

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026
Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

June 19, 2026
Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.