Kasar Sin ta bayyana adawa tare da Allah wadai, game da hare-hare kan fararen hula da kayayyakin more rayuwa a Sudan, tana fatan za a tsagaita bude wuta nan ba da jimawa ba a kasar.
A baya-bayan nan an kai wasu hare-hare da jirage marasa matuka kan muhimman wurare a Port Sudan dake gabar tekun Bahr Maliya a gabashin kasar, lamarin da ya lalata filin jirgin sama da tashar ruwa.
Game da wannan batu ne kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ta bayyana kiran kasar ga dukkan bangarori, da su tabbatar da tsaron fararen hula da kayayyakin more rayuwa.
Ta ce, kasar Sin ba ta goyon bayan wani bangare a rikicin na Sudan. Kuma tana fatan za a dakatar da yaki a kasar nan ba da jimawa ba, domin rage matsalolin jin kai da samun ci gaba a tsarin siyasa da dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali da ci gaba a kasar, nan ba da jimawa ba. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp