• English
  • Business News
Saturday, May 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Na Fatan Amurka Za Ta Girmama Ka’idojin Takara Bisa Adalci

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Na Fatan Amurka Za Ta Girmama Ka’idojin Takara Bisa Adalci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta ce, nan ba da jimawa ba, za ta yi karin haske game da ziyarar sakataren harkokin wajen Amurka a kasar Sin. 

Kakakin ma’aikatar Wang Wenbin ne ya bayyana haka a yau, yayin taron manema labarai da aka saba yi a kullum, bayan an nemi jin ta bakinsa game da tsokacin da sakataren harkokin wajen Amurka Anthony Blinken ya yi yayin ziyararsa a Shanghai. Wang Wenbin ya bayyana cewa, sun riga sun gabatar da makasudin ziyarar jami’in na Amurka, kwanaki biyun da suka gabata, tare kuma da bayyana matsayin kasar Sin kan batun.

  • Xi Ya Yi Kira Ga Chongqing Da Ya Rubuta Nasa Tarihi Cikin Aikin Zamanantar Da Kasar Sin
  • Kasar Sin Ta Bayyana Tarin Rarar Da Take Da Shi Ta Albarkartun Mai Da Iskar Gas

Kakakin ya kara da cewa, kasar Sin ta kasance mai aiwatar da hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya bisa ka’idojin kasuwa, haka kuma ta kasance mai nacewa ga tsarin cinikayya tsakanin bangarori da dama da kuma aiwatar da ka’idojin hukumar kula da cinikayya ta duniya (WTO) yadda ya kamata. A cewarsa, ana fata bangaren Amurka zai martaba ka’idojin takara bisa adalci da biyayya ga ka’idojin WTO da hada hannu da kasar Sin wajen samar da kyakkyawan yanayin raya dangantakar tattalin arziki da cinikayya dake tsakaninsu cikin aminci.

Har ila yau, Wang Wenbin ya bayyana cewa, kasar Sin ta samar da tallafi mai yawa na yaki da cutar cizon sauro ta Malaria ga kasa da kasa, ta hanyar amfani da maganin Artemisinin wajen samar da magunguna da tallafin kwararru da ginin cibiyoyin yaki da cutar da horar da jami’ai. Ya ce, a nahiyar Afrika, shirye-shiryen yaki da cutar da magunguna da dabarun kasar Sin, sun samar da fatan rayuwa ga mutanen nahiyar da dake fama da cutar. Ya kara da cewa, kasar Sin na dogaro da cibiyar bincike da horo kan kawar da cutar Malaria ta MDD, wajen horar da sama da jami’an lafiya da masana 2,000 daga kasashe da yankuna 85, game da kandagarki da takaita cutar Malaria da sauran cututtuka masu yaduwa. A cewar hukumar lafiya ta duniya (WHO), kimanin mutane miliyan 240 a yankin kudu da hamadar Sahara kadai, sun amfana da hadin maganin Artemisinin.

Haka zalika, Wang Wenbin, ya ce ci gaba da yaki a Gaza, abu ne da ba za a lamunta ba, kuma kisan gillar da ake wa yara da mata, abu ne da ba za a yi hakuri da shi ba, haka kuma ba za a taba amincewa da kawo tsaiko ga yunkurin Kwamitin Sulhu na MDD na ingiza tsagaita bude wuta ba. Kasar Sin na bukatar kasashe masu ruwa da tsaki, su daina kawo tsaiko kan matakan Kwamitin Sulhun, tare da kira ga bangarorin da batun ya shafa su aiwatar da kudurin Kwamitin Sulhun mai lamba 2728, da cimma tsagaita bude wuta mai dorewa nan take kuma ba tare da gindaya sharadi ba. Bugu da kari a tabbatar da samar da agajin jin kai mai dorewa ba tare da katsewa ba, domin kawo karshen wahalhalun da al’ummar Palasdinu ke fuskanta da daina kunyata wayewar kan bil Adama. (Fa’iza Mustapha)

Labarai Masu Nasaba

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Za Mu Fahimci Kuskuren Amurka Na Cewa Wai Kasar Sin “Ta Wuce Gona Da Iri” Wajen Samar Da Hajoji

Next Post

Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Samar Ya Wuce Misali Ko Damuwar Amurka Ta Wuce Kima?

Related

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal
Daga Birnin Sin

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

6 hours ago
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

7 hours ago
CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU
Daga Birnin Sin

CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU

9 hours ago
Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman

10 hours ago
Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara

11 hours ago
Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba

11 hours ago
Next Post
Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Samar Ya Wuce Misali Ko Damuwar Amurka Ta Wuce Kima?

Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Samar Ya Wuce Misali Ko Damuwar Amurka Ta Wuce Kima?

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

May 16, 2025
Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

May 16, 2025
JAMB Ta Ƙaddamar Da Binciken Gaggawa Kan Sakamakon Jarrabawar Bana Bayan Jerin Ƙorafe-Ƙorafe 

JAMB Ta Ƙaddamar Da Binciken Gaggawa Kan Sakamakon Jarrabawar Bana Bayan Jerin Ƙorafe-Ƙorafe 

May 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya

May 16, 2025
CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU

CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU

May 16, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ƙwato Shanun Sata 1,000 A Taraba

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ƙwato Shanun Sata 1,000 A Taraba

May 16, 2025
Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman

Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara

Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara

May 16, 2025
Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba

Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba

May 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.