• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Na Fatan Amurka Za Ta Girmama Ka’idojin Takara Bisa Adalci

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Na Fatan Amurka Za Ta Girmama Ka’idojin Takara Bisa Adalci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta ce, nan ba da jimawa ba, za ta yi karin haske game da ziyarar sakataren harkokin wajen Amurka a kasar Sin. 

Kakakin ma’aikatar Wang Wenbin ne ya bayyana haka a yau, yayin taron manema labarai da aka saba yi a kullum, bayan an nemi jin ta bakinsa game da tsokacin da sakataren harkokin wajen Amurka Anthony Blinken ya yi yayin ziyararsa a Shanghai. Wang Wenbin ya bayyana cewa, sun riga sun gabatar da makasudin ziyarar jami’in na Amurka, kwanaki biyun da suka gabata, tare kuma da bayyana matsayin kasar Sin kan batun.

  • Xi Ya Yi Kira Ga Chongqing Da Ya Rubuta Nasa Tarihi Cikin Aikin Zamanantar Da Kasar Sin
  • Kasar Sin Ta Bayyana Tarin Rarar Da Take Da Shi Ta Albarkartun Mai Da Iskar Gas

Kakakin ya kara da cewa, kasar Sin ta kasance mai aiwatar da hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya bisa ka’idojin kasuwa, haka kuma ta kasance mai nacewa ga tsarin cinikayya tsakanin bangarori da dama da kuma aiwatar da ka’idojin hukumar kula da cinikayya ta duniya (WTO) yadda ya kamata. A cewarsa, ana fata bangaren Amurka zai martaba ka’idojin takara bisa adalci da biyayya ga ka’idojin WTO da hada hannu da kasar Sin wajen samar da kyakkyawan yanayin raya dangantakar tattalin arziki da cinikayya dake tsakaninsu cikin aminci.

Har ila yau, Wang Wenbin ya bayyana cewa, kasar Sin ta samar da tallafi mai yawa na yaki da cutar cizon sauro ta Malaria ga kasa da kasa, ta hanyar amfani da maganin Artemisinin wajen samar da magunguna da tallafin kwararru da ginin cibiyoyin yaki da cutar da horar da jami’ai. Ya ce, a nahiyar Afrika, shirye-shiryen yaki da cutar da magunguna da dabarun kasar Sin, sun samar da fatan rayuwa ga mutanen nahiyar da dake fama da cutar. Ya kara da cewa, kasar Sin na dogaro da cibiyar bincike da horo kan kawar da cutar Malaria ta MDD, wajen horar da sama da jami’an lafiya da masana 2,000 daga kasashe da yankuna 85, game da kandagarki da takaita cutar Malaria da sauran cututtuka masu yaduwa. A cewar hukumar lafiya ta duniya (WHO), kimanin mutane miliyan 240 a yankin kudu da hamadar Sahara kadai, sun amfana da hadin maganin Artemisinin.

Haka zalika, Wang Wenbin, ya ce ci gaba da yaki a Gaza, abu ne da ba za a lamunta ba, kuma kisan gillar da ake wa yara da mata, abu ne da ba za a yi hakuri da shi ba, haka kuma ba za a taba amincewa da kawo tsaiko ga yunkurin Kwamitin Sulhu na MDD na ingiza tsagaita bude wuta ba. Kasar Sin na bukatar kasashe masu ruwa da tsaki, su daina kawo tsaiko kan matakan Kwamitin Sulhun, tare da kira ga bangarorin da batun ya shafa su aiwatar da kudurin Kwamitin Sulhun mai lamba 2728, da cimma tsagaita bude wuta mai dorewa nan take kuma ba tare da gindaya sharadi ba. Bugu da kari a tabbatar da samar da agajin jin kai mai dorewa ba tare da katsewa ba, domin kawo karshen wahalhalun da al’ummar Palasdinu ke fuskanta da daina kunyata wayewar kan bil Adama. (Fa’iza Mustapha)

Labarai Masu Nasaba

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Za Mu Fahimci Kuskuren Amurka Na Cewa Wai Kasar Sin “Ta Wuce Gona Da Iri” Wajen Samar Da Hajoji

Next Post

Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Samar Ya Wuce Misali Ko Damuwar Amurka Ta Wuce Kima?

Related

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro
Daga Birnin Sin

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

16 minutes ago
Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK
Daga Birnin Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

20 hours ago
Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan

21 hours ago
Sin Na Gaggauta Gina Tsarin Tattalin Arziki Mai Kiyaye Muhallin Halittu
Daga Birnin Sin

Sin Na Gaggauta Gina Tsarin Tattalin Arziki Mai Kiyaye Muhallin Halittu

22 hours ago
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
Daga Birnin Sin

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

2 days ago
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

2 days ago
Next Post
Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Samar Ya Wuce Misali Ko Damuwar Amurka Ta Wuce Kima?

Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Samar Ya Wuce Misali Ko Damuwar Amurka Ta Wuce Kima?

LABARAI MASU NASABA

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

August 11, 2025
Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

August 11, 2025
Borno

‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno

August 11, 2025
Yajin aiki

Kungiyoyin Kwadago Sun Tsunduma Yajin Aiki A Taraba

August 11, 2025
Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19

Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19

August 11, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

August 11, 2025
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

August 10, 2025
Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

August 10, 2025
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

August 10, 2025
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.