Ma’aikatar harkokin kudi ta kasar Sin, ta ce kasar ta ware jimilar yuan miliyan 105, kwatankwacin dala miliyan 14.7 domin tallafawa gaggauta gyaran titunan da ambaliyar ruwa ta lalata.
Ma’aikatar ta bayyana a jiya cewa, za a yi amfani da kudin nan take, domin gyara titunan da suka lalace sanadiyyar ambaliya a lardunan Guangdong da Guangxi da Zhejiang da Fujian da Jiangxi da Hunan da kuma Guizhou, tare da tabbatar da zirga-zirga cikin aminci yayin da ake cikin lokacin ambaliya.
Yankunan kudancin kasar Sin da dama na fama da zubar ruwan sama akai-akai a wannan lokacin zafi na bana, lamarin da ya haifar da lalacewar tituna da gine-gine, tare da rutsawa da mutane. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp