• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Afirka Na Fadada Cudanya Da Kasar Sin A Fannoni Daban Daban

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasashen Afirka Na Fadada Cudanya Da Kasar Sin A Fannoni Daban Daban
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ga duk mai bibiyar harkokin da suka shafi cudanyar kasar Sin da kasashen Afirka musamman a shekarar 2023 da ta gabata, ba zai rasa ganin muhimman nasarori da sassan biyu suka cimma a fannin yaukaka dangankata, da cimma moriya tare ba. 

Karkashin dandalin bunkasa hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka na FOCAC, da manufofin bunkasa ci gaban duniya, da na wanzar da tsaron kasa da kasa, da shawarar wayewar kan duniya, tare da karfafa matakan gina shawarar “ziri daya da hanya daya” ko BRI da Sin ta gabatar, an kai ga cimma manyan nasarori masu fa’idar gaske.

  • Xi Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Iran Bisa Munanan Hare-haren Ta’addanci Da Aka Kai A Kasar
  • Jarin Sin Ya Bunkasa Sashen Sabbin Makamashi A Zimbabwe

A baya-bayan nan, mun ga yadda hadin gwiwa tsakanin Sin da Habasha ke kara samun tagomashi a fannonin cinikayya, da zuba jari, da samar da manyan ababen more rayuwa, da noma da sadarwa. Sauran sun hada da fannin raya al’adu, da ilimi, da musaya tsakanin al’ummun sassan biyu da sauransu, wanda hakan ya haifar da moriya mai tarin yawa ga jama’ar kasashen biyu.

A bana kuma, ana sa ran aiwatar da matakai daban daban na daga matsayin dangantakar Sin da Habasha bisa mutunta juna, da fadada tattaunawa tsakanin jami’ai, ta yadda za a gudu tare a tsira tare.

Baya ga Habasha, ita ma kasar Tunisiya ta karbi bakuncin taron musaya a fannin wayewar kai na hadin gwiwa da kasar Sin, taron da ya gudana a farkon makon jiya a birnin Tunis.

Labarai Masu Nasaba

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

An jiyo wasu daga manyan baki mahalarta taron na bayyana shi a matsayin dama ta musaya, da tattaunawa game da wayewar kan Sin da Tunisiya, wanda zai ingiza ci gaban bai daya, da wadata tsakanin kasashen biyu.

Kaza lika, wasu masharhanta na ganin shawarar Sin ta ingiza wayewar kan duniya, wadda ke fatan ganin an samu zaman jituwa da koyi daga nasarorin juna tsakanin wayewar kai daban daban, karkashin taruka masu kama da irin wanda aka shirya a birnin Tunis, zai taimaka matuka wajen bunkasa wayewar kan daukacin bil adama.

Yayin da Sin da Tunisiya ke samun karin tagomashi a fannin bunkasa dangantaka, da yadda Sin din ke fadada cudanya da Habasha, sauran kasashen Afirka ma na bin wannan tafarki, na cin gajiya, tare kasa mafi girma a jerin kasashe masu tasowa wato kasar Sin, musamman a shekarun baya bayan nan.

Fatan dai shi ne kamar yadda aka raya kyakkyawar dangantaka tsakanin kasashen Afirka da Sin a shekarar 2023 da ta shude, hakan zai dore a bana wato shekarar 2024, zuwa shekaru da dama a nan gaba, ta yadda tafiya tsakanin Sin da kawayenta kasashe masu tasowa za ta dore har abada. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

AFCON 2023: Kasar Da Ta Lashe Gasar Kofin Afirka Za Ta Samu Kyautar Naira Biliyan 6.53

Next Post

CMG Ya Gabatar Da Dandamali 4 Na Nuna Shirin Talibijin Na Murnar Sabuwar Shekarar 2024 Bisa Kalandar Gargajiyar Kasar Sin 

Related

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan
Daga Birnin Sin

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

2 hours ago
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

3 hours ago
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5
Daga Birnin Sin

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

4 hours ago
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu
Daga Birnin Sin

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

5 hours ago
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani
Daga Birnin Sin

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

6 hours ago
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya
Daga Birnin Sin

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

1 day ago
Next Post
CMG Ya Gabatar Da Dandamali 4 Na Nuna Shirin Talibijin Na Murnar Sabuwar Shekarar 2024 Bisa Kalandar Gargajiyar Kasar Sin 

CMG Ya Gabatar Da Dandamali 4 Na Nuna Shirin Talibijin Na Murnar Sabuwar Shekarar 2024 Bisa Kalandar Gargajiyar Kasar Sin 

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.