• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Duniya Na Kara Zuba Jari A Kasar Sin

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasashen Duniya Na Kara Zuba Jari A Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da kasar Sin ta samu bunkasuwar zuba jari daga ketare a wannan shekarar dake daf da karewa, kafofin watsa labaru na kasashen yammacin duniya suna ci gaba da yin amfani da tsofaffin dabaru wajen sukar yanayin kasuwanci da tattalin arzikin kasar Sin.  

Idan kana bibiyar sabbin labarai kan tattalin arzikin kasar Sin ko jarin waje a shafukan yanar gizo na kafofin watsa labaru na kasashen yamma, na tabbata za ka gano wasu labarai marasa dadi game da yanayin tattalin arzikin kasar ko kuma jarin waje.

  • An Wallafa Littafin Xi Jinping Game Da BRI Bugun Shekarar 2023
  • An Fara Gina Cibiyar UHD Highland Ta CMG

Maganar gaskiya ita ce yawancin wadannan labarun ba daidai ba ne. Kasar Sin ta inganta yanayin kasuwancin kasar akai-akai tun farkon shekarar 2023 lokacin da ta bullo da matakai da dama don daidaita zuba jarin waje, wanda ya jawo karin kamfanonin waje zuba jari a kasar Sin, wanda kuma ke nuni da yadda tattalin arzikin Sin ke kara bunkasuwa cikin sauri.

Wani bincike da Faransa ta gudanar ya nuna cewa, yadda kasar Sin ta kara yawan jarinta na waje kai tsaye wato FDI, ya kara wa masu zuba jari kwarin gwiwa game da halin da tattalin arzikin kasar ke ciki, lamarin da ya sa wasu manazarta ke hasashen cewa, kamfanonin kasa da kasa sun yanke shawarar “karfafa kasuwancinsu a kasar Sin”, a cewar wani binciken da hukumar hidimar kudi wato “BNP Paribas Asset Management” ta Faransa ta yi.

Kasar Sin ta zama cibiyar zuba jarin kasashen waje saboda yanayin tattalin arzikinta dake maraba da kamfanonin kasashen waje. Ma’aikatar kasuwancin kasar Sin ta bayyana cewa, a cikin watanni 10 na farkon shekarar 2023, an kafa sabbin kamfanoni 41,947 da suka zuba jari a kasashen waje, lamarin da ya nuna babban ci gaban da aka samu da kashi 32 cikin 100 na jarin waje kai tsaye (FDI). FDI cikin kasar Sin ya karu da kashi 110.3, kashi 94.6, kashi 90, kashi 66.1, da kashi 33 cikin dari daga kasashen Canada, Birtaniya, Faransa, Switzerland, da Netherlands bi da bi. Wannan karuwar na da nasaba da yadda kamfanoni na kasa da kasa suke son zuba jari a kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

Bugu da kari, jarin waje da fannin masana’antu ya samu ya kai Yuan biliyan 283.44 na kasar Sin, wanda ya nuna karuwar kashi 1.9 cikin dari idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata. Na’am, wannan labari ne mai ban sha’awa, la’akari da munanan bayanai da wasu kafafen yada labarai na kasa da kasa ke yadawa game da daidaituwar tattalin arzikin kasar Sin. Bayanan nasu ba su da tasiri yayin da saka hannun jari na yau da kullun na kamfanonin ketare ke karuwa. (Muhammed Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IndiaSinXi Jinping
ShareTweetSendShare
Previous Post

NNL: An Ci Tarar Kungiyar Mailantarki FC Naira Miliyan Daya Kan Rashin Da’a

Next Post

Zaben Cike Gurbi: APC Za Ta Sayar Da Takardar Tsayawa Takarar Sanata Naira Miliyan 20

Related

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

14 hours ago
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington
Daga Birnin Sin

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

15 hours ago
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela
Daga Birnin Sin

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

16 hours ago
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli
Daga Birnin Sin

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

17 hours ago
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

18 hours ago
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

19 hours ago
Next Post
APC

Zaben Cike Gurbi: APC Za Ta Sayar Da Takardar Tsayawa Takarar Sanata Naira Miliyan 20

LABARAI MASU NASABA

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

August 22, 2025
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

August 22, 2025
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

August 22, 2025
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

August 22, 2025
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

August 22, 2025
Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

August 22, 2025
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

August 22, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

August 22, 2025
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.