• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Duniya Na Kara Zuba Jari A Kasar Sin

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasashen Duniya Na Kara Zuba Jari A Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da kasar Sin ta samu bunkasuwar zuba jari daga ketare a wannan shekarar dake daf da karewa, kafofin watsa labaru na kasashen yammacin duniya suna ci gaba da yin amfani da tsofaffin dabaru wajen sukar yanayin kasuwanci da tattalin arzikin kasar Sin.  

Idan kana bibiyar sabbin labarai kan tattalin arzikin kasar Sin ko jarin waje a shafukan yanar gizo na kafofin watsa labaru na kasashen yamma, na tabbata za ka gano wasu labarai marasa dadi game da yanayin tattalin arzikin kasar ko kuma jarin waje.

  • An Wallafa Littafin Xi Jinping Game Da BRI Bugun Shekarar 2023
  • An Fara Gina Cibiyar UHD Highland Ta CMG

Maganar gaskiya ita ce yawancin wadannan labarun ba daidai ba ne. Kasar Sin ta inganta yanayin kasuwancin kasar akai-akai tun farkon shekarar 2023 lokacin da ta bullo da matakai da dama don daidaita zuba jarin waje, wanda ya jawo karin kamfanonin waje zuba jari a kasar Sin, wanda kuma ke nuni da yadda tattalin arzikin Sin ke kara bunkasuwa cikin sauri.

Wani bincike da Faransa ta gudanar ya nuna cewa, yadda kasar Sin ta kara yawan jarinta na waje kai tsaye wato FDI, ya kara wa masu zuba jari kwarin gwiwa game da halin da tattalin arzikin kasar ke ciki, lamarin da ya sa wasu manazarta ke hasashen cewa, kamfanonin kasa da kasa sun yanke shawarar “karfafa kasuwancinsu a kasar Sin”, a cewar wani binciken da hukumar hidimar kudi wato “BNP Paribas Asset Management” ta Faransa ta yi.

Kasar Sin ta zama cibiyar zuba jarin kasashen waje saboda yanayin tattalin arzikinta dake maraba da kamfanonin kasashen waje. Ma’aikatar kasuwancin kasar Sin ta bayyana cewa, a cikin watanni 10 na farkon shekarar 2023, an kafa sabbin kamfanoni 41,947 da suka zuba jari a kasashen waje, lamarin da ya nuna babban ci gaban da aka samu da kashi 32 cikin 100 na jarin waje kai tsaye (FDI). FDI cikin kasar Sin ya karu da kashi 110.3, kashi 94.6, kashi 90, kashi 66.1, da kashi 33 cikin dari daga kasashen Canada, Birtaniya, Faransa, Switzerland, da Netherlands bi da bi. Wannan karuwar na da nasaba da yadda kamfanoni na kasa da kasa suke son zuba jari a kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Bugu da kari, jarin waje da fannin masana’antu ya samu ya kai Yuan biliyan 283.44 na kasar Sin, wanda ya nuna karuwar kashi 1.9 cikin dari idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata. Na’am, wannan labari ne mai ban sha’awa, la’akari da munanan bayanai da wasu kafafen yada labarai na kasa da kasa ke yadawa game da daidaituwar tattalin arzikin kasar Sin. Bayanan nasu ba su da tasiri yayin da saka hannun jari na yau da kullun na kamfanonin ketare ke karuwa. (Muhammed Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IndiaSinXi Jinping
ShareTweetSendShare
Previous Post

NNL: An Ci Tarar Kungiyar Mailantarki FC Naira Miliyan Daya Kan Rashin Da’a

Next Post

Zaben Cike Gurbi: APC Za Ta Sayar Da Takardar Tsayawa Takarar Sanata Naira Miliyan 20

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

12 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

12 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

14 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

17 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

18 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

20 hours ago
Next Post
APC

Zaben Cike Gurbi: APC Za Ta Sayar Da Takardar Tsayawa Takarar Sanata Naira Miliyan 20

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.