ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Duniya Na Kara Zuba Jari A Kasar Sin

by CGTN Hausa
3 years ago
Duniya

Yayin da kasar Sin ta samu bunkasuwar zuba jari daga ketare a wannan shekarar dake daf da karewa, kafofin watsa labaru na kasashen yammacin duniya suna ci gaba da yin amfani da tsofaffin dabaru wajen sukar yanayin kasuwanci da tattalin arzikin kasar Sin.  

Idan kana bibiyar sabbin labarai kan tattalin arzikin kasar Sin ko jarin waje a shafukan yanar gizo na kafofin watsa labaru na kasashen yamma, na tabbata za ka gano wasu labarai marasa dadi game da yanayin tattalin arzikin kasar ko kuma jarin waje.

  • An Wallafa Littafin Xi Jinping Game Da BRI Bugun Shekarar 2023
  • An Fara Gina Cibiyar UHD Highland Ta CMG

Maganar gaskiya ita ce yawancin wadannan labarun ba daidai ba ne. Kasar Sin ta inganta yanayin kasuwancin kasar akai-akai tun farkon shekarar 2023 lokacin da ta bullo da matakai da dama don daidaita zuba jarin waje, wanda ya jawo karin kamfanonin waje zuba jari a kasar Sin, wanda kuma ke nuni da yadda tattalin arzikin Sin ke kara bunkasuwa cikin sauri.

ADVERTISEMENT

Wani bincike da Faransa ta gudanar ya nuna cewa, yadda kasar Sin ta kara yawan jarinta na waje kai tsaye wato FDI, ya kara wa masu zuba jari kwarin gwiwa game da halin da tattalin arzikin kasar ke ciki, lamarin da ya sa wasu manazarta ke hasashen cewa, kamfanonin kasa da kasa sun yanke shawarar “karfafa kasuwancinsu a kasar Sin”, a cewar wani binciken da hukumar hidimar kudi wato “BNP Paribas Asset Management” ta Faransa ta yi.

Kasar Sin ta zama cibiyar zuba jarin kasashen waje saboda yanayin tattalin arzikinta dake maraba da kamfanonin kasashen waje. Ma’aikatar kasuwancin kasar Sin ta bayyana cewa, a cikin watanni 10 na farkon shekarar 2023, an kafa sabbin kamfanoni 41,947 da suka zuba jari a kasashen waje, lamarin da ya nuna babban ci gaban da aka samu da kashi 32 cikin 100 na jarin waje kai tsaye (FDI). FDI cikin kasar Sin ya karu da kashi 110.3, kashi 94.6, kashi 90, kashi 66.1, da kashi 33 cikin dari daga kasashen Canada, Birtaniya, Faransa, Switzerland, da Netherlands bi da bi. Wannan karuwar na da nasaba da yadda kamfanoni na kasa da kasa suke son zuba jari a kasar Sin.

LABARAI MASU NASABA

An Yi Babban Taro Kan Tsarin Shugabancin Duniya A Bangaren AI A Shanghai

Dalibai 4 Da Ke Wakiltar Kasar Sin A Gasar Kasa Da Kasa Ta Chemistry Olympiad Sun Lashe Lambobin Zinare

Bugu da kari, jarin waje da fannin masana’antu ya samu ya kai Yuan biliyan 283.44 na kasar Sin, wanda ya nuna karuwar kashi 1.9 cikin dari idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata. Na’am, wannan labari ne mai ban sha’awa, la’akari da munanan bayanai da wasu kafafen yada labarai na kasa da kasa ke yadawa game da daidaituwar tattalin arzikin kasar Sin. Bayanan nasu ba su da tasiri yayin da saka hannun jari na yau da kullun na kamfanonin ketare ke karuwa. (Muhammed Yahaya)

Duniya
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ra’ayin Sin Game Da AI Mai Mayar Da Hankali Kan Bukatun Dan Adam Ya Samu Goyon Bayan Kasa Da Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

MASU ALAKA

An Yi Babban Taro Kan Tsarin Shugabancin Duniya A Bangaren AI A Shanghai
Daga Birnin Sin

An Yi Babban Taro Kan Tsarin Shugabancin Duniya A Bangaren AI A Shanghai

July 20, 2026
Dalibai 4 Da Ke Wakiltar Kasar Sin A Gasar Kasa Da Kasa Ta Chemistry Olympiad Sun Lashe Lambobin Zinare
Daga Birnin Sin

Dalibai 4 Da Ke Wakiltar Kasar Sin A Gasar Kasa Da Kasa Ta Chemistry Olympiad Sun Lashe Lambobin Zinare

July 20, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso
Daga Birnin Sin

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

July 19, 2026
Next Post
APC

Zaben Cike Gurbi: APC Za Ta Sayar Da Takardar Tsayawa Takarar Sanata Naira Miliyan 20

LABARAI MASU NASABA

Cikakken Jerin Yan Wasan Da Suka Lashe Kyautuka A Gasar Kofin Duniya

Cikakken Jerin Yan Wasan Da Suka Lashe Kyautuka A Gasar Kofin Duniya

July 20, 2026
Sojoji Sun Kama Wani Ɗan Sudan Da Ake Zargi Da Haɗa Kai Da ’Yan Ta’adda A Borno

Sojoji Sun Kama Wani Ɗan Sudan Da Ake Zargi Da Haɗa Kai Da ’Yan Ta’adda A Borno

July 20, 2026
Matashi Ya Mutu, Wasu Da Dama Sun Jikkata Yayin Murnar Lashe Kofin Duniya Da Spain Ta Yi

Matashi Ya Mutu, Wasu Da Dama Sun Jikkata Yayin Murnar Lashe Kofin Duniya Da Spain Ta Yi

July 20, 2026
Mbappé Ya Zama Mafi Yawan Ƙwallaye A Tarihin Gasar Kofin Duniya

Mbappé Ya Zama Mafi Yawan Ƙwallaye A Tarihin Gasar Kofin Duniya

July 20, 2026
An Yi Babban Taro Kan Tsarin Shugabancin Duniya A Bangaren AI A Shanghai

An Yi Babban Taro Kan Tsarin Shugabancin Duniya A Bangaren AI A Shanghai

July 20, 2026
Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin ISWAP Na Sace Ɗalibai A Borno, Sun Ceto 46

Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin ISWAP Na Sace Ɗalibai A Borno, Sun Ceto 46

July 19, 2026
Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi

Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi

July 19, 2026
Dalibai 4 Da Ke Wakiltar Kasar Sin A Gasar Kasa Da Kasa Ta Chemistry Olympiad Sun Lashe Lambobin Zinare

Dalibai 4 Da Ke Wakiltar Kasar Sin A Gasar Kasa Da Kasa Ta Chemistry Olympiad Sun Lashe Lambobin Zinare

July 20, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

July 19, 2026
NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

July 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.