• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Ghana Da Kenya Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Labarai
0
Kasashen Ghana Da Kenya Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kasar Ghana, Nana Akufo-Addo da na Kenya, William Ruto, sun shaida hakan inda Ministar harkokin wajen Ghana, Shirley Ayorkor Botchwey, da sakataren majalisar ministocin harkokin wajen Kenya, Dokta Musalia Mudabadi, suka jagoranci rattaba hannun.

Kasar Ghana da Kenya sun kara habaka huldar diplomasiyya da tattalin arziki, ta hanyar rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna da za ta tabbatar da hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu da burin nemo hanyoyin da kasashen za su bunkasa huldar kasuwanci, tattalin arziki da zamantakewa a tsakaninsu.

  • An Bude Baje Kolin Kayayyakin Masarufi Na Kasa Da Kasa Na Sin Karo Na 4
  • Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Daga Da Kaso 5% A Rubu’in Farko Na Bana

Kasashen biyu sun rattaba hannu kan wasu yarjeniyoyi 7 da suka hada da ilimi, yawon bude ido, tsaro, da inganta zuba jari, masana’antu, kere-kere da kasuwanci, a yayin ziyarar kwanaki uku da shugaban kasar Kenya, William Ruto, ya kai zuwa Ghana.

Shugaban Kasar Ghana, Nana Akufo-Addo da na Kenya, William Ruto, sun shaida hakan inda Ministar harkokin wajen Ghana, Shirley Ayorkor Botchwey, da sakataren majalisar ministocin harkokin wajen Kenya, Dokta Musalia Mudabadi, suka jagoranci rattaba hannu kan yarjejeniyar diflomasiya a fadar Shugaban Kasa, Jubilee House, dake Birnin Accra.

Haka kuma an rattaba hannu kan wasu yarjeniyoyi da suka hada da ilimi, yawon bude ido, hadin gwiwa kan tsaro, kasuwanci da zuba jari, masana’antu da gudanar da mulki domin karfafa alakar dake tsakanin kasashen biyu.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

A wani taron manema labarai na hadin gwiwa, shugaba Akufo-Addo ya ce, ‘Huldar kasuwanci da tattalin arziki tana ci gaba da bunkasa a tsakanin kasashen Ghana da Kenya, inda kasashen biyu ke kara fahimtar juna da kuma nuna goyon baya ga juna a kungiyoyin kasa da kasa da suka hada da Majalisar Dinkin Duniya, Tarayyar Afirka, da Kungiyar Kasashen Renon Ingila, na Commonwealth’.

A nasa bangaren Shugaba Ruto ya bayyana cewa, ‘yancin zirga-zirgar jama’a tsakanin Ghana da Kenya ya haifar da fa’ida sosai a fannin kasuwanci, zuba jari, da kuma yawon bude ido.

“A dangane da haka, ni da mai girma shugaban kasa, mun lura cewa, kasuwanci tsakanin Kenya da Ghana ya bunkasa a shekarar 2022, misali, a shekarar 2022, Kayayyakin da Kenya ta shigo da su cikin Ghana sun kai na Dalar Amurka miliyan 10.4, kuma an kiyasta wasu kayayyakin da ake shigo da su a kan Dalar Amurka miliyan 4.8.”

Wani mai sharhi kan harkokin siyasar cikin gida da ketare, Malam Issah Abdul Salam yace,sakamakon alaka da aka dora tsakanin Ghana da Kenya, ya sa shugaba William Ruto ya zo Ghana don kara jaddada alaka mai kyau da ke tsakaninsu tun da jimawa. Kuma wannan ziyarar za ta aka kara bunkasa sha’anin, ‘ilimi, yawon bude ido da ba da dama ga ziyarar kasashen juna, abubuwa ne da za su samar da mafani masu dimbin yawa tsakanin Ghana da Kenya”.

Masani kan harkokin kudi da kasuwanci, Hamza Attijjany, ya ce kasashen biyu za su amfana ta bangaren tattalin arziki, musamman a kasuwanci da bas hi da shinge tsakanin kasashen Africa, da kasar Ghana da Kenya suka runguma da hannu biyu-biyu.

Ya ce, ‘A lokacin da kasar Kenya ta fara yin batir, Ghana ce kasa ta farko da aka fara yi wa talla don kasuwanci. Lallai Ghana da Kenya za su samu ci gaban tattalin arziki da ma nahiyar Afirka baki daya’.

Al’ummar kasashen biyu, za su samu alfanu idan an tabbatar da wadannan yarjejeniyoyin, in ji mai sharhi kan al’amuran yau da kullum, Malam Issah Mairago Gibril Abbas,wanda ya ce daliban kasashen biyu za su samu damar zurfafa iliminsu ta hanyar yarjejeniyar; haka kuma ‘yan kasuwar kasashen za su ci moriyar shirin nan na cinikayya tsakanin kasashen Afrika mara shinge AfCFTA.

A yayin ziyarar shugaba Ruto, ta kwanaki ukun, ya ba da lecca a shalkwatar AfCFTA ya kuma ziyarci kabarin tsohon shugaban Ghana, Kwame Nkrumah, a Birnin Accra. Daga bisani Ghana ta karrama shi da babbar karramawa mai daraja, wato Companion of the Order of the Star of the Bolta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wacce Kungiya Ce Za Ta Iya Lashe Gasar Firimiya?

Next Post

Jinyar Wata 7: Babu Abin Da Zan Ce Ga Masoyana Sai Godiya -Malam Na Ta’ala

Related

Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC
Labarai

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

4 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

5 hours ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

6 hours ago
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya
Labarai

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

7 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

9 hours ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

9 hours ago
Next Post
Jinyar Wata 7: Babu Abin Da Zan Ce Ga Masoyana Sai Godiya -Malam Na Ta’ala

Jinyar Wata 7: Babu Abin Da Zan Ce Ga Masoyana Sai Godiya -Malam Na Ta'ala

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.