ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Ghana Da Kenya Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Ghana

Shugaban Kasar Ghana, Nana Akufo-Addo da na Kenya, William Ruto, sun shaida hakan inda Ministar harkokin wajen Ghana, Shirley Ayorkor Botchwey, da sakataren majalisar ministocin harkokin wajen Kenya, Dokta Musalia Mudabadi, suka jagoranci rattaba hannun.

Kasar Ghana da Kenya sun kara habaka huldar diplomasiyya da tattalin arziki, ta hanyar rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna da za ta tabbatar da hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu da burin nemo hanyoyin da kasashen za su bunkasa huldar kasuwanci, tattalin arziki da zamantakewa a tsakaninsu.

  • An Bude Baje Kolin Kayayyakin Masarufi Na Kasa Da Kasa Na Sin Karo Na 4
  • Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Daga Da Kaso 5% A Rubu’in Farko Na Bana

Kasashen biyu sun rattaba hannu kan wasu yarjeniyoyi 7 da suka hada da ilimi, yawon bude ido, tsaro, da inganta zuba jari, masana’antu, kere-kere da kasuwanci, a yayin ziyarar kwanaki uku da shugaban kasar Kenya, William Ruto, ya kai zuwa Ghana.

ADVERTISEMENT

Shugaban Kasar Ghana, Nana Akufo-Addo da na Kenya, William Ruto, sun shaida hakan inda Ministar harkokin wajen Ghana, Shirley Ayorkor Botchwey, da sakataren majalisar ministocin harkokin wajen Kenya, Dokta Musalia Mudabadi, suka jagoranci rattaba hannu kan yarjejeniyar diflomasiya a fadar Shugaban Kasa, Jubilee House, dake Birnin Accra.

Haka kuma an rattaba hannu kan wasu yarjeniyoyi da suka hada da ilimi, yawon bude ido, hadin gwiwa kan tsaro, kasuwanci da zuba jari, masana’antu da gudanar da mulki domin karfafa alakar dake tsakanin kasashen biyu.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

A wani taron manema labarai na hadin gwiwa, shugaba Akufo-Addo ya ce, ‘Huldar kasuwanci da tattalin arziki tana ci gaba da bunkasa a tsakanin kasashen Ghana da Kenya, inda kasashen biyu ke kara fahimtar juna da kuma nuna goyon baya ga juna a kungiyoyin kasa da kasa da suka hada da Majalisar Dinkin Duniya, Tarayyar Afirka, da Kungiyar Kasashen Renon Ingila, na Commonwealth’.

A nasa bangaren Shugaba Ruto ya bayyana cewa, ‘yancin zirga-zirgar jama’a tsakanin Ghana da Kenya ya haifar da fa’ida sosai a fannin kasuwanci, zuba jari, da kuma yawon bude ido.

“A dangane da haka, ni da mai girma shugaban kasa, mun lura cewa, kasuwanci tsakanin Kenya da Ghana ya bunkasa a shekarar 2022, misali, a shekarar 2022, Kayayyakin da Kenya ta shigo da su cikin Ghana sun kai na Dalar Amurka miliyan 10.4, kuma an kiyasta wasu kayayyakin da ake shigo da su a kan Dalar Amurka miliyan 4.8.”

Wani mai sharhi kan harkokin siyasar cikin gida da ketare, Malam Issah Abdul Salam yace,sakamakon alaka da aka dora tsakanin Ghana da Kenya, ya sa shugaba William Ruto ya zo Ghana don kara jaddada alaka mai kyau da ke tsakaninsu tun da jimawa. Kuma wannan ziyarar za ta aka kara bunkasa sha’anin, ‘ilimi, yawon bude ido da ba da dama ga ziyarar kasashen juna, abubuwa ne da za su samar da mafani masu dimbin yawa tsakanin Ghana da Kenya”.

Masani kan harkokin kudi da kasuwanci, Hamza Attijjany, ya ce kasashen biyu za su amfana ta bangaren tattalin arziki, musamman a kasuwanci da bas hi da shinge tsakanin kasashen Africa, da kasar Ghana da Kenya suka runguma da hannu biyu-biyu.

Ya ce, ‘A lokacin da kasar Kenya ta fara yin batir, Ghana ce kasa ta farko da aka fara yi wa talla don kasuwanci. Lallai Ghana da Kenya za su samu ci gaban tattalin arziki da ma nahiyar Afirka baki daya’.

Al’ummar kasashen biyu, za su samu alfanu idan an tabbatar da wadannan yarjejeniyoyin, in ji mai sharhi kan al’amuran yau da kullum, Malam Issah Mairago Gibril Abbas,wanda ya ce daliban kasashen biyu za su samu damar zurfafa iliminsu ta hanyar yarjejeniyar; haka kuma ‘yan kasuwar kasashen za su ci moriyar shirin nan na cinikayya tsakanin kasashen Afrika mara shinge AfCFTA.

A yayin ziyarar shugaba Ruto, ta kwanaki ukun, ya ba da lecca a shalkwatar AfCFTA ya kuma ziyarci kabarin tsohon shugaban Ghana, Kwame Nkrumah, a Birnin Accra. Daga bisani Ghana ta karrama shi da babbar karramawa mai daraja, wato Companion of the Order of the Star of the Bolta.

Ghana
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
Jinyar Wata 7: Babu Abin Da Zan Ce Ga Masoyana Sai Godiya -Malam Na Ta’ala

Jinyar Wata 7: Babu Abin Da Zan Ce Ga Masoyana Sai Godiya -Malam Na Ta'ala

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.