• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Yamma Suna Tsotse Jinin ‘Yan Afirka Yayin Da Kasar Sin Ke Kawo Bege

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasashen Yamma Suna Tsotse Jinin ‘Yan Afirka Yayin Da Kasar Sin Ke Kawo Bege
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana wawushe albarkatun Kasa da ma’adinai, ana kwace ’yancin mallakar kasa, ana zaluntar mutane. Wannan ita ce mummunar fahimta da da’awar da kafofin yada labarai na kasashen yamma suke yadawa game da shirin shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya ko BRI a takaice. A wajensu, BRI na nufin “farauta” da “tsangwama.”

An ce wanzami ba ya son jarfa, a hakikanin gaskiya wannan kage da kasashen yamma suka yiwa shirin BRI da nufin muzgunawa kasar Sin na bayyana ainihin illoli wadanda suka hada da mamaya, katsalandan, tsangwama da babakeren da Amurka da kawayenta na yamma suka yiwa kasashen Afirka ne.

  • Ganawa Da Xi Jinping: Ina Godiya Gare Shi Bisa Cimma Burina
  • Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Zai Halarci Bikin Bude Taron BRF

Bari mu kawo wasu misalai sa’annan mu kwatanta bangarorin biyu, za mu fahimci wace kasa ce ke “farautar Afirka da tsangwama mata” tsakanin kasar Sin da Amurka da kawayenta na yamma. Kasar Amurka ta kafa sansanonin sojoji 29 a nahiyar Afirka yayin da kasar Sin take da daya a Djibouti. Amma duk da haka Amurka na ikirarin cewa Sin ce ke yin katsalandan a nahiyar.

Gaskiya ne cewa kasar Sin na gina layin dogo a duk fadin Afirka wanda Joe Biden shugaban ƙasar Amurka ya yi mafarkin cewa Amurka za ta gina, a maimakon haka, shugabannin na Amurka sai tofin Allah wadai da ayyukan Sinawa a Afirka suke ke yi, alhalin a duk ziyararsu a Afirka alal akalli sai sun sauka a wani filin jirgin saman Afirka da Sin ta gina, su kuma shiga cikin gari a kan wata babbar hanyar da kasar Sin ta shimfida. Wannan shi ne ake ce ma munafurcin dodo ya kan ci mai shi.

To wai shin mene ne shisshigi kuma mene ne ci gaba? Kasar Sin ta shiga Afirka lungu da sako tana taimakawa wajen gina ababen more rayuwa da Turawan mulkin mallaka ba su taba ginawa ba, da kuma taimakawa wajen gina makomar tattalin arziki mai cin gashin kanta bayan mulkin mallaka, wanda kasashen yammacin duniya suka yi duk mai yiwuwa don hanawa.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

Kasar Sin ba ta bautar da kowa a Afirka ba kuma kasar Sin ba ta mamaye ko’ina a Afirka ba. Amma babu wata kasa a nahiyar Afirka da kasashen yamma ba su debi magabatanmu a matsayin bayi zuwa kasashensu suka bautar da su ba. Kana, babu wani inchin murabba’i na kasa da mulkin mallakar yamma bai mamaye ba.

Wane ne ya taba kashe shugabannin kasashen Afirka? Kasar Sin ba ta yi juyin mulki ba a Afirka. Hasali ma, Sin ba ta tsoma baki a harkar shugabancin kasashen waje, wannan ka’ida ce ta Sin. Ba sai na tunashe mu ta’adin da kasar Amurka ta aikata a kasar Libya zuwa Timbuktu, ko kasar Laberiya zuwa Congo ba.

Kasar Sin ba ta taba goyon bayan wariyar launin fata a Rhodesia da Afirka ta Kudu ba. Sabanin haka, kasar Sin ta goyi bayan gwagwarmayar ‘yanci a dukkan bangarorin biyu. Yamma ce ta rura wutar fitinar wariyar launin fata da ta samu tushe a tarihin kasashen biyu.

Ba kasar Sin ce ta karya farashin Uranium na Nijar zuwa wajen Yuro 0.1 kan ko wane kilogiram ba, a lokacin da farashin a kasuwa ya kai wajen Yuro 25 kan kowane kilogiram na Uranium daga Nijar. Har ila yau, wannan shi ma makircin yamma ne.

Shirin shawarar “ziri daya da hanya daya” na kasar Sin yana shimfida hanyoyin mota, layin dogo da habaka sufurin jiragen sama, da gina makarantu, asibitoci, jami’o’i da makarantun kananan yara.

Su kuma kasashen yamma na totse jinin ’yan Afirka kamar yadda suka yi shekaru aru-aru da suka gabata, yayin da kasar Sin ke kawo bege. Wannan shi ne bambanci tsakanin Sin da kasashen Yamma. (Muhammed Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaSinXi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shawarar BRI Ta Kawo Manyan Sauye-sauye A Duniya Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

Next Post

NIS Ta Shirya Taro A Kan Alfanun Tattalin Arzikin Teku Ga Manyan ‘Yan Kasuwa A Ribas

Related

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

10 hours ago
Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi
Daga Birnin Sin

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

11 hours ago
Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba
Daga Birnin Sin

Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

11 hours ago
Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar

11 hours ago
Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025

13 hours ago
Gwamnatin Sin: Gwamnatin Jama’a Domin Jama’a
Daga Birnin Sin

Gwamnatin Sin: Gwamnatin Jama’a Domin Jama’a

13 hours ago
Next Post
Nis

NIS Ta Shirya Taro A Kan Alfanun Tattalin Arzikin Teku Ga Manyan 'Yan Kasuwa A Ribas

LABARAI MASU NASABA

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

August 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

August 6, 2025
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

August 6, 2025
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

August 5, 2025
Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

August 5, 2025
Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

August 5, 2025
Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

August 5, 2025
Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

August 5, 2025
Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar

Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar

August 5, 2025
Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

August 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.